Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad, ya rushe kwamitin gudanarwar ƙungiyar kwallon ƙafa ta Wikki Tourists nan take, bayan rashin taɓuka abun arziki da ƙungiyar ta yi a kakar wasan 2025/2026 ta Gasar Firimiya ta Nijeriya (NPFL), wanda ya janyo faɗuwarta zuwa Gasar Nijeriya ta NNL.
Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Mukhtar Gidado, ya fitar a daren ranar Alhamis.
Sanarwar ta bayyana cewa gwamnan ya amince da rushe kwamitin ne bayan nazari mai zurfi kan yadda ƙungiyar ta taka leda a kakar wasa da kuma matakan da gwamnatin jihar ta ɗauka domin tabbatar da ta ci gaba da kasancewa a babbar gasar kwallon kafa ta ƙasar.
Ya ce wannan mataki na nuna kudirin gwamnatin jihar na sake farfaɗo da Wikki Tourists, dawo da amincewar jama’a kan yadda ake tafiyar da ƙungiyar, tare da shimfiɗa ingantaccen tubali domin dawowarta cikin gaggawa zuwa babbar gasar kwallon kafa ta Nijeriya.
Sanarwar ta ƙara da cewa, a tsawon kakar wasan, gwamnatin jihar ta bai wa ƙungiyar dukkanin tallafin kuɗi da na gudanarwa da ake buƙata domin kara mata karfin gasa da inganta kwazonzo, amma kash sai ta Ka-sa-ka-sau.
Sanarwar ta kuma bayyana cewa, a matsayin matakin ƙarshe na ƙoƙarin kauce wa faɗuwa daga gasar, gwamnati ta kafa Kwamitin Ceto (Rescue Team) a karshen kakar wasan domin ya haɗa kai da kwamitin gudanarwa wajen ceto ƙungiyar.
“Abin takaici, duk da waɗannan matakai, ba a samu sakamakon da ake buƙata ba, inda daga ƙarshe ƙungiyar ta fadi zuwa Gasar Nijeriya ta kasa (NNL),” in ji sanarwar.
Saboda haka, Gwamna Bala Mohammed ya amince da naɗin tsohon daraktan wasanni na Jihar Bauchi, Alhaji Haruna Bako, a matsayin mai kula da ƙungiyar na wucin hadi (Interim Sole Administrator), har sai an kafa sabon kwamitin gudanarwa na dindindin.
Sanarwar ta ce ana sa ran sabon mai kula da ƙungiyar zai karɓi ragamar gudanarwa nan take, amsar ragamar kula da dukkan ayyuka, ƙadarori, takardu da kuma alhakin ƙungiyar, tare da fara ɗaukar matakan da za su sake farfaɗo da ƙungiyar domin samun kyakkyawan sakamako da kuma shiri mai inganci a kakar Gasar Nijeriya ta ƙasa mai zuwa.
Gwamnatin Jihar Bauchi ta kuma nuna godiyarta ga kwamitin gudanarwar da aka kora ƙarƙashin jagorancin Salmanu Abubakar bisa gudummawar da ya bayar ga ƙungiyar, tare da yi musu fatan alheri a dukkan ayyukansu na gaba.
Gwamnatin ta sake jaddada ƙudirinta na farfaɗo da Kungiyar Kwallon Kafa ta Wikki Tourists, tana mai tabbatar wa magoya bayanta cewa za a ɗauki dukkan matakan da suka dace domin mayar da kungiyar cikin manyan kungiyoyin kwallon kafa na Nijeriya da kuma tabbatar da dawowarta cikin gaggawa zuwa Gasar Firimiya ta Nijeriya (NPFL).













