ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
46 minutes ago
Wikki

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad, ya rushe kwamitin gudanarwar ƙungiyar kwallon ƙafa ta Wikki Tourists nan take, bayan rashin taɓuka abun arziki da ƙungiyar ta yi a kakar wasan 2025/2026 ta Gasar Firimiya ta Nijeriya (NPFL), wanda ya janyo faɗuwarta zuwa Gasar Nijeriya ta NNL.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Mukhtar Gidado, ya fitar a daren ranar Alhamis.

Sanarwar ta bayyana cewa gwamnan ya amince da rushe kwamitin ne bayan nazari mai zurfi kan yadda ƙungiyar ta taka leda a kakar wasa da kuma matakan da gwamnatin jihar ta ɗauka domin tabbatar da ta ci gaba da kasancewa a babbar gasar kwallon kafa ta ƙasar.

ADVERTISEMENT

Ya ce wannan mataki na nuna kudirin gwamnatin jihar na sake farfaɗo da Wikki Tourists, dawo da amincewar jama’a kan yadda ake tafiyar da ƙungiyar, tare da shimfiɗa ingantaccen tubali domin dawowarta cikin gaggawa zuwa babbar gasar kwallon kafa ta Nijeriya.

Sanarwar ta ƙara da cewa, a tsawon kakar wasan, gwamnatin jihar ta bai wa ƙungiyar dukkanin tallafin kuɗi da na gudanarwa da ake buƙata domin kara mata karfin gasa da inganta kwazonzo, amma kash sai ta Ka-sa-ka-sau.

LABARAI MASU NASABA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Sanarwar ta kuma bayyana cewa, a matsayin matakin ƙarshe na ƙoƙarin kauce wa faɗuwa daga gasar, gwamnati ta kafa Kwamitin Ceto (Rescue Team) a karshen kakar wasan domin ya haɗa kai da kwamitin gudanarwa wajen ceto ƙungiyar.

“Abin takaici, duk da waɗannan matakai, ba a samu sakamakon da ake buƙata ba, inda daga ƙarshe ƙungiyar ta fadi zuwa Gasar Nijeriya ta kasa (NNL),” in ji sanarwar.

Saboda haka, Gwamna Bala Mohammed ya amince da naɗin tsohon daraktan wasanni na Jihar Bauchi, Alhaji Haruna Bako, a matsayin mai kula da ƙungiyar na wucin hadi (Interim Sole Administrator), har sai an kafa sabon kwamitin gudanarwa na dindindin.

Sanarwar ta ce ana sa ran sabon mai kula da ƙungiyar zai karɓi ragamar gudanarwa nan take, amsar ragamar kula da dukkan ayyuka, ƙadarori, takardu da kuma alhakin ƙungiyar, tare da fara ɗaukar matakan da za su sake farfaɗo da ƙungiyar domin samun kyakkyawan sakamako da kuma shiri mai inganci a kakar Gasar Nijeriya ta ƙasa mai zuwa.

Gwamnatin Jihar Bauchi ta kuma nuna godiyarta ga kwamitin gudanarwar da aka kora ƙarƙashin jagorancin Salmanu Abubakar bisa gudummawar da ya bayar ga ƙungiyar, tare da yi musu fatan alheri a dukkan ayyukansu na gaba.

Gwamnatin ta sake jaddada ƙudirinta na farfaɗo da Kungiyar Kwallon Kafa ta Wikki Tourists, tana mai tabbatar wa magoya bayanta cewa za a ɗauki dukkan matakan da suka dace domin mayar da kungiyar cikin manyan kungiyoyin kwallon kafa na Nijeriya da kuma tabbatar da dawowarta cikin gaggawa zuwa Gasar Firimiya ta Nijeriya (NPFL).

Wikki
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
Wikki
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • Sulaiman
    Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
  • Sulaiman
    Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya
  • Sulaiman
    Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

MASU ALAKA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Wasanni

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Next Post
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.