Babbar Kotun Tarayya da ke Jihar Kano ta yanke wa wani matashi mai shekaru 28, Ashiru Idris, hukuncin ɗaurin shekaru bakwai a gidan yari bisa laifin tallata da kuma neman sayar da wiwi ta kafafen sada zumunta.
Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA) ta ce an kama Ashiru Idris ne a ranar 22 ga watan Afrilu, 2026, bayan wani bidiyonsa da ke tallata wiwi ya bazu a kafafen sada zumunta.
Mai shari’a S.M. Shuaibu ya same shi da laifi tare da umartar cewa hukuncin ɗaurin ya fara aiki daga ranar 14 ga watan Yuli, 2026.
NDLEA ta bayyana hukuncin a matsayin gargaɗi ga duk masu amfani da kafafen sada zumunta wajen tallata ko sayar da miyagun ƙwayoyi.
Hukumar ta kuma ce za ta ci gaba da cafke tare da gurfanar da masu aikata irin waɗannan laifuka.













