ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tserewar Likitocin Nijeriya Zuwa Kasashen Waje

by Leadership Hausa and Sulaiman
1 year ago
Likitocin Nijeriya

Kafafen yada labaran kasar nan sun cika da rahotanni kala-kala kwanan nan inda suka bayyana cewa, Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da kaddamar da wasu tsare-tsare da za su dakatar da ficewar da Likitoci, ma’aikatan lafiyar Nijeriya ke yi zuwa kasashen waje.Ana ganin wannan wani martani ne na yadda aka cigaba da samun Likitocin Nijeriya ke tserewa zuwa kasashen waje domin samun rayuwa ta-gari da albashi mai tsoka musamman a kasashe irinsu Amurka, Turai da kuma Saudiyya.

 

Wadannan sabon tsare-tsaren da gwamnati ta fito da su, sun yi hannun riga da manufar gwamnati a baya, inda ta ke karfafa likitoci su fita zuwa kasashen waje domin neman ingantacciyar rayuwa ta kansu da iyalansu. Saboda wannan tsarin ne, Farfesa Isaac Adewole, wanda shi kan shi farfesa ne na harkar lafiya kuma tsohon shugaban jami’ar Ibadan ne, a lokacin yana Ministan Lafiya a karkashin gwamnatin Muhammadu Buhari, ya taba yin kira ga Likitocin Nijeriya da su rungumi aikin noma a matsayin wata hanyar nishadantar da kan su da kuma matsayin maganin kukan da suke yawan yi na rashin isasshen albashi da sauran alawu-alawus.

ADVERTISEMENT
  • Binciken LEADERSHIP Hausa… Asalin Abin Da Ya Faru Da Iyalan Da Suka Mutu Sanadin Gurbataccen Abinci
  • Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Bayan wannan katobarar, sai gashi kuma wani minista a gamnatin na Muhammadu Buhar, ministan kwadago, Dr Chris Ngige, wanda shima likita ne,ya yi ikirarin cewa, NIjeriya na da isasshun likitoci da za su iya bai wa wasu kasashen rarar likitocin da suka rage, amma kuma hakikanin gaskiya ba haka lamarin yake ba.Hakanan shi ma mai ba shugaba Buhari shawara a bangaren harkar yada labarai, Femi Adesina, ya goyi bayan wadannan shawarwarin inda ya ce, shi bai ga matsalar da fitar likitocin take haifarwa ba, domin kuwa hakan na taimakawa wajen kara kwarewar likitocinmu su samu irin kwarewar da ba za su iya samu a cikin Nijeriya ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

In har za a yi wa wadannan jami’an gwamnatin adalci, lalle babu wani laifi ga ma’aikatan lafiya su nemi wata hanyar gudanar da rayuwa baya ga harkar da suka samu horo a kai ta likitanci. Musamman ganin an taba samun wani shugaban bankin duniya mai suna Jim Yong Kim, wanda babban likita ne shaharre.A gwamnatin Buhari, Okechukwu Enelamah wanda ministan ciniki da zuba jari ne amma kuma cikakken likita ne da ya fada cikin harkokin kasuwanci. Amma kuma abin da ya kamata a lura a nan shi ne wadannan sun kauce wa harkar kiwon lafiya ne a matsayin zabin kansu ba wai sun kauce ba ne sadoda rashin jin dadin aiki a matsayin likita a Nijeriya.

 

A ra’ayinmu, wadannan maganganun na manyan kuma jami’an gwamnati su ne manyan dalilan da suka sa likitocin Nijeriya suka fara kaura zuwa kasashen waje. A tsokacinsa, Sakataren Gwaamnatin tayarayya a zamanin mulkin Shugaba kasa Buhari, Boss Mustapha, ya bayyana cewa bai san tsananin karancin likitoci a kasar nan ya kai lamarin da ya gani ba a lokacin cutar Korona.A kan haka ya fahimci cewa, lalle ya kamata a dauki matakan dakile ficewar likitocinmu da suke yi zuwa kasashen waje.

 

Kamar dai sauran bangarorin rayuwar Nijeriya, mahukunta sun yi watsi da harkar kiwon lafiya da yadda ake gudanar da ita a asibitocinmu, sun yi watsi da yadda ake gudanar da harkokin kula da lafiyar al’umma a asibitoci.Wannan kuma da gangan ne suka yi hakan domin wadannan mahukunta na tafiya kasashen waje ne domin kulawa da lafiyar su da ta iyalansu,wannan matakin kuma ya taimaka wajen tsotse kudaden ajiyar kasa na kasashen waje. Cin hanci da rashawa sun taimaka wajen tatse kudaden da aka ware domin kulawa da bangaren kiwon lafiya.

 

Ta haka ne kayan aiki na zamani suka yi karanci a asibitocinmu,inda harkar kiwon lafiya ta koma bangaren masu zaman kansu, inda su kuma suka dora ta, a harkokinsu saboda neman riba, hakan kuma ya sa talakawan da basu da kudi daga samun ingantacciyar kiwon lafiya saboda rashin kudi.

 

A bayyane lamarin yake,a wasu lokutta, Likitoci a asibitocin gwamnati zaka ga suna sayen safar hannun wadda suke amfani da ita wajen duba marasa lafiya.Duk da muhimmancin wadannan kayan aiki ba a samu a asibitoci domin amfani Likita. Wannan kadai sun isa ya ba mutum cikakken sanin halin da fannin lafiya yake ciki.A ra’ayinmu karin abin da ke kara mastalar da Likitocin Nijeriya suke fuskanta su ne yawan aiki da kuma rashin ingantacen albashi.Halin tabarbarewar asibitocin Nijeriya ya ke karfafa masu karbar aiki daga kasashen waje da zarar an yi masu tayi.

 

Daga wadannan hujjojin ne, muka yi garo da duk wani mataki na hana Likitoci cika burinsu na aiki a wasu wuraren domin sun yi karo da dokokin kasa da na kasashen waje, wadanda suka samar da ‘yancin rayuwa a ko’ina a fadin duniya matukar mutum ya cika ka’idojin da aka tsara.Sai dai irin likitocin nan da gwamnnati ta horas ta kuma shiga wata yarjejeniya da su, in ba haka ba, to haramun ne neman dakatar da kowa, ba ma Likitoci kawai ba daga fita kasashen waje don neman ingantacciyar rayuwa.

 

Maimakon sanya wasu dokokin da za su takura fitar Likitoci kasashen waje, ya kamata gwamnati ta lura da bangarorin da ke bukatar gyara domin ta inganta su musamman abin da suka shafi kayan aiki albashi da jin dadin likitoci gaba daya da kuma kudaden giratuti in Likita ya bar fagen aiki.

 

Hakanan kuma dole gwamnati ta dakatar da shirin nan na tura manyan jami’anta kasashen waje domin duba lafiyarsu. Kudaden da ake zubawa domin wannan tafiyar neman lafiya sai a tura su domin samar da cikakkun kayan aiki a asibitocinmu

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Ra'ayinmu

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

October 17, 2025
Likitocin Nijeriya
Ra'ayinmu

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Fyade
Ra'ayinmu

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

September 7, 2025
Next Post
Gwamnatin Kano Za Ta Tsara Zamantar Da Magungunan Gargajiya

Gwamnatin Kano Za Ta Tsara Zamantar Da Magungunan Gargajiya

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025
Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

November 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025
Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.