ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tserewar Likitocin Nijeriya Zuwa Kasashen Waje

by Leadership Hausa and Sulaiman
2 years ago
Likitocin Nijeriya

Kafafen yada labaran kasar nan sun cika da rahotanni kala-kala kwanan nan inda suka bayyana cewa, Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da kaddamar da wasu tsare-tsare da za su dakatar da ficewar da Likitoci, ma’aikatan lafiyar Nijeriya ke yi zuwa kasashen waje.Ana ganin wannan wani martani ne na yadda aka cigaba da samun Likitocin Nijeriya ke tserewa zuwa kasashen waje domin samun rayuwa ta-gari da albashi mai tsoka musamman a kasashe irinsu Amurka, Turai da kuma Saudiyya.

 

Wadannan sabon tsare-tsaren da gwamnati ta fito da su, sun yi hannun riga da manufar gwamnati a baya, inda ta ke karfafa likitoci su fita zuwa kasashen waje domin neman ingantacciyar rayuwa ta kansu da iyalansu. Saboda wannan tsarin ne, Farfesa Isaac Adewole, wanda shi kan shi farfesa ne na harkar lafiya kuma tsohon shugaban jami’ar Ibadan ne, a lokacin yana Ministan Lafiya a karkashin gwamnatin Muhammadu Buhari, ya taba yin kira ga Likitocin Nijeriya da su rungumi aikin noma a matsayin wata hanyar nishadantar da kan su da kuma matsayin maganin kukan da suke yawan yi na rashin isasshen albashi da sauran alawu-alawus.

ADVERTISEMENT
  • Binciken LEADERSHIP Hausa… Asalin Abin Da Ya Faru Da Iyalan Da Suka Mutu Sanadin Gurbataccen Abinci
  • Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Bayan wannan katobarar, sai gashi kuma wani minista a gamnatin na Muhammadu Buhar, ministan kwadago, Dr Chris Ngige, wanda shima likita ne,ya yi ikirarin cewa, NIjeriya na da isasshun likitoci da za su iya bai wa wasu kasashen rarar likitocin da suka rage, amma kuma hakikanin gaskiya ba haka lamarin yake ba.Hakanan shi ma mai ba shugaba Buhari shawara a bangaren harkar yada labarai, Femi Adesina, ya goyi bayan wadannan shawarwarin inda ya ce, shi bai ga matsalar da fitar likitocin take haifarwa ba, domin kuwa hakan na taimakawa wajen kara kwarewar likitocinmu su samu irin kwarewar da ba za su iya samu a cikin Nijeriya ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

In har za a yi wa wadannan jami’an gwamnatin adalci, lalle babu wani laifi ga ma’aikatan lafiya su nemi wata hanyar gudanar da rayuwa baya ga harkar da suka samu horo a kai ta likitanci. Musamman ganin an taba samun wani shugaban bankin duniya mai suna Jim Yong Kim, wanda babban likita ne shaharre.A gwamnatin Buhari, Okechukwu Enelamah wanda ministan ciniki da zuba jari ne amma kuma cikakken likita ne da ya fada cikin harkokin kasuwanci. Amma kuma abin da ya kamata a lura a nan shi ne wadannan sun kauce wa harkar kiwon lafiya ne a matsayin zabin kansu ba wai sun kauce ba ne sadoda rashin jin dadin aiki a matsayin likita a Nijeriya.

 

A ra’ayinmu, wadannan maganganun na manyan kuma jami’an gwamnati su ne manyan dalilan da suka sa likitocin Nijeriya suka fara kaura zuwa kasashen waje. A tsokacinsa, Sakataren Gwaamnatin tayarayya a zamanin mulkin Shugaba kasa Buhari, Boss Mustapha, ya bayyana cewa bai san tsananin karancin likitoci a kasar nan ya kai lamarin da ya gani ba a lokacin cutar Korona.A kan haka ya fahimci cewa, lalle ya kamata a dauki matakan dakile ficewar likitocinmu da suke yi zuwa kasashen waje.

 

Kamar dai sauran bangarorin rayuwar Nijeriya, mahukunta sun yi watsi da harkar kiwon lafiya da yadda ake gudanar da ita a asibitocinmu, sun yi watsi da yadda ake gudanar da harkokin kula da lafiyar al’umma a asibitoci.Wannan kuma da gangan ne suka yi hakan domin wadannan mahukunta na tafiya kasashen waje ne domin kulawa da lafiyar su da ta iyalansu,wannan matakin kuma ya taimaka wajen tsotse kudaden ajiyar kasa na kasashen waje. Cin hanci da rashawa sun taimaka wajen tatse kudaden da aka ware domin kulawa da bangaren kiwon lafiya.

 

Ta haka ne kayan aiki na zamani suka yi karanci a asibitocinmu,inda harkar kiwon lafiya ta koma bangaren masu zaman kansu, inda su kuma suka dora ta, a harkokinsu saboda neman riba, hakan kuma ya sa talakawan da basu da kudi daga samun ingantacciyar kiwon lafiya saboda rashin kudi.

 

A bayyane lamarin yake,a wasu lokutta, Likitoci a asibitocin gwamnati zaka ga suna sayen safar hannun wadda suke amfani da ita wajen duba marasa lafiya.Duk da muhimmancin wadannan kayan aiki ba a samu a asibitoci domin amfani Likita. Wannan kadai sun isa ya ba mutum cikakken sanin halin da fannin lafiya yake ciki.A ra’ayinmu karin abin da ke kara mastalar da Likitocin Nijeriya suke fuskanta su ne yawan aiki da kuma rashin ingantacen albashi.Halin tabarbarewar asibitocin Nijeriya ya ke karfafa masu karbar aiki daga kasashen waje da zarar an yi masu tayi.

 

Daga wadannan hujjojin ne, muka yi garo da duk wani mataki na hana Likitoci cika burinsu na aiki a wasu wuraren domin sun yi karo da dokokin kasa da na kasashen waje, wadanda suka samar da ‘yancin rayuwa a ko’ina a fadin duniya matukar mutum ya cika ka’idojin da aka tsara.Sai dai irin likitocin nan da gwamnnati ta horas ta kuma shiga wata yarjejeniya da su, in ba haka ba, to haramun ne neman dakatar da kowa, ba ma Likitoci kawai ba daga fita kasashen waje don neman ingantacciyar rayuwa.

 

Maimakon sanya wasu dokokin da za su takura fitar Likitoci kasashen waje, ya kamata gwamnati ta lura da bangarorin da ke bukatar gyara domin ta inganta su musamman abin da suka shafi kayan aiki albashi da jin dadin likitoci gaba daya da kuma kudaden giratuti in Likita ya bar fagen aiki.

 

Hakanan kuma dole gwamnati ta dakatar da shirin nan na tura manyan jami’anta kasashen waje domin duba lafiyarsu. Kudaden da ake zubawa domin wannan tafiyar neman lafiya sai a tura su domin samar da cikakkun kayan aiki a asibitocinmu

Likitocin Nijeriya
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe
Likitocin Nijeriya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Ra'ayinmu

Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

May 15, 2026
Next Post
Gwamnatin Kano Za Ta Tsara Zamantar Da Magungunan Gargajiya

Gwamnatin Kano Za Ta Tsara Zamantar Da Magungunan Gargajiya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.