• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wajibi Ne Amurka Ta Cika Alkawarinta

by CMG Hausa
3 years ago
in Labarai
0
Wajibi Ne Amurka Ta Cika Alkawarinta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A daren 28 ga wannan wata ne, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya tattauna da takwaransa na kasar Amurka Joe Biden ta wayar tarho, inda ya yi bayani kan nauyin da ke bisa wuyan kasashen Sin da Amurka, ya kuma yi nuni da cewa, Amurka ta yi kuskuren fahimtar dangantakar da ke tsakanin Sin da Amurka da kuma bunkasuwar kasar Sin, sa’an nan ya bayyana matsayin kasar Sin kan batun Taiwan.

A nasa bangaren, Biden ya bayyana fatansa na neman hada kai a tsakanin Amurka da Sin, da daidaita sabani yadda ya kamata, ya kuma yi alkawarin cewa, Amurka ba ta sauya kuma ba za ta sauya manufar “kasar Sin daya tak a duniya” ba, ba kuma ta goyon bayan ‘yancin Taiwan.

  • An Tattauna Tsakanin Shugaba Xi Na Sin Da Biden Na Amurka

Wannan ne karo na 5 da shugabannin Sin da Amurka suka tattauna da juna ta wayar tarho, tun bayan Biden ya zama shugaban Amurka.

Kana kuma, tattaunawar da shugabannin 2 suka yi a wannan karo, tana da matukar muhimmanci a wannan muhimmin lokaci. Yanzu haka yaduwar annobar cutar COVID-19 da rikicin Ukraine sun kawo tsaiko ga batutuwan ci gaba da kuma tsaro.

Yayin da kasashen duniya suke fuskantar sauye-sauye da matsaloli, suna fatan Sin da Amurka za su daidaita sabanin dake tsakaninsu yadda ya kamata, za kuma su ba da jagora wajen kiyaye zaman lafiya da tsaro a duniya da kara azama kan bunkasar duniya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

An lura da cewa, a wannan karo, shugaba Xi ya mai da hankali wajen yin bayani kan matsayin kasar Sin game da batun Taiwan, wanda shi ne mafi muhimmanci da kuma jawo hankali a fannin huldar da ke tsakanin Sin da Amurka.

Baya ga haka, a halin yanzu ana kara fuskantar barazana a mashigin tekun Taiwan sakamakon wutar da Amurka take ta rurawa.

Wajibi ne Amurka ta fahimci cewa, idan ba ta tinkari batun Taiwan yadda ya kamata ba, to, za a yi illata huldar da ke tsakanin Sin da Amurka, wadda ba a taba ganin irinta ba.

Amurka ta sha yin alwashin martaba manufar “kasar Sin daya tak a duniya”, da rashin goyon bayan ‘yancin Taiwan, to, wajibi ne ta cika alkawarinta. (Tasallah Yuan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

Next Post

Ziyarar Kabarin Annabi SAW (3)

Related

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

20 minutes ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

1 hour ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

5 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

6 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

15 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

17 hours ago
Next Post
Ziyarar Kabarin Annabi SAW (2)

Ziyarar Kabarin Annabi SAW (3)

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.