• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wajibi Ne Amurka Ta Cika Alkawarinta

by CMG Hausa
3 years ago
Amurka

A daren 28 ga wannan wata ne, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya tattauna da takwaransa na kasar Amurka Joe Biden ta wayar tarho, inda ya yi bayani kan nauyin da ke bisa wuyan kasashen Sin da Amurka, ya kuma yi nuni da cewa, Amurka ta yi kuskuren fahimtar dangantakar da ke tsakanin Sin da Amurka da kuma bunkasuwar kasar Sin, sa’an nan ya bayyana matsayin kasar Sin kan batun Taiwan.

A nasa bangaren, Biden ya bayyana fatansa na neman hada kai a tsakanin Amurka da Sin, da daidaita sabani yadda ya kamata, ya kuma yi alkawarin cewa, Amurka ba ta sauya kuma ba za ta sauya manufar “kasar Sin daya tak a duniya” ba, ba kuma ta goyon bayan ‘yancin Taiwan.

  • An Tattauna Tsakanin Shugaba Xi Na Sin Da Biden Na Amurka

Wannan ne karo na 5 da shugabannin Sin da Amurka suka tattauna da juna ta wayar tarho, tun bayan Biden ya zama shugaban Amurka.

Kana kuma, tattaunawar da shugabannin 2 suka yi a wannan karo, tana da matukar muhimmanci a wannan muhimmin lokaci. Yanzu haka yaduwar annobar cutar COVID-19 da rikicin Ukraine sun kawo tsaiko ga batutuwan ci gaba da kuma tsaro.

Yayin da kasashen duniya suke fuskantar sauye-sauye da matsaloli, suna fatan Sin da Amurka za su daidaita sabanin dake tsakaninsu yadda ya kamata, za kuma su ba da jagora wajen kiyaye zaman lafiya da tsaro a duniya da kara azama kan bunkasar duniya.

LABARAI MASU NASABA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An lura da cewa, a wannan karo, shugaba Xi ya mai da hankali wajen yin bayani kan matsayin kasar Sin game da batun Taiwan, wanda shi ne mafi muhimmanci da kuma jawo hankali a fannin huldar da ke tsakanin Sin da Amurka.

Baya ga haka, a halin yanzu ana kara fuskantar barazana a mashigin tekun Taiwan sakamakon wutar da Amurka take ta rurawa.

Wajibi ne Amurka ta fahimci cewa, idan ba ta tinkari batun Taiwan yadda ya kamata ba, to, za a yi illata huldar da ke tsakanin Sin da Amurka, wadda ba a taba ganin irinta ba.

Amurka ta sha yin alwashin martaba manufar “kasar Sin daya tak a duniya”, da rashin goyon bayan ‘yancin Taiwan, to, wajibi ne ta cika alkawarinta. (Tasallah Yuan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati
Labarai

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba
Labarai

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Next Post
Ziyarar Kabarin Annabi SAW (2)

Ziyarar Kabarin Annabi SAW (3)

LABARAI MASU NASABA

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.