Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Ya Dace Buhari Ya Sa Ido Kan Aikin Hanyar Abuja-Kano – Sakataren ‘Yan Lemo

by Muhammad
February 4, 2021
in LABARAI
2 min read
Abuja Kaduna
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Isa Abdullahi Gidan ‘Bakko,

Ana ci gaba da nanata kira ga shugaban kasa Muhammadu Buhari day a kara sa ido na yadda ake yin aikin hanyar da ta taso daga Abuja zuwa Kano, domin kawo karshen rasa rayuka da ake yi dare da rana da kuma yadda ‘yan baya ga dangi ke aiwatar da muggan ayyuka da suka hada da garkuwa da mutane da fashi da makami da kuma kisar gilla da ke faruwa a wannan hanya,

samndaads

Wannan kira ta fito ne daga bakin babban sakataren kungiyar ‘yan Lemo reshen kananan hukumomin Sabon gari da kuma Zariya Ustas Ahmad Dayyab Ya Salam,a lokacin day a amsa tambayoyin wakilinmu da ke Zariya.kan matsalolin da suke faruwa a wannan hanyar da aka ambata.

Ustas Ahmad Dayyab ya ci gaba da cewar, ga duk wanda ke mu’amala da wannan hanyar da ta taso daga Abuja zuwa Kaduna , a cewarsa , da zarar mutum ya fara tafiya daga Abuja zuwa Kaduna ko daga Abuja zuwa Kaduna ba shi da kwanciyar hankali sai fa mutum ya isa Abuja ko kuma isa garin Kaduna, kamar yadda ya ce a nan ne zai numfasa.

A cewarsa, lokaci ya yi da shugaban kasa da kansa zai sa ido a wannan hanya, tun da wadanda ya danka ma su amanar sa ido kan yadda ake yin aikin hanyar, alamu sun nuna ba sa bayyana ma sa gaskiyar matsalolin da suke faruwa a wannan hanya, da kowa ya yi amannar ta zama tarkon mutuwa ga wadanda bin hanyar dare da kuma rana.

Da kuma ya juya ga yadda lalacewar hanyar da kuma tafiyar hawainiya na yadda aikin ke tafiya, Ustas Ya Salam hya nunar da cewar, su da ke sana’ar Lemo, lalacewar hanyar ta shafe su na yadda, yadda motocin da suke dauko ma su Lemo daga kudancin Nijeriya zuwa arewa, su na shafe awanni ma su yawa, sabanin lokutan da suke dauka zuwa arewacin Nijeriya, kafin hanyar ta sami matsalolin da aka ambata.

Ya ci gaba da cewar, lokaci ya yi da  za a duba wannan hanya da al’umma za su sami sa’ida, tare da kawo karshen matsalolin da suke faruwa a hanyar na rasa rayuka da kisar gilla da kuma fashi da makami da ke faruwa a kan hanyar dare da kuma rana.

A karshe Ustas Ahmad Dayyab Ya Salam babban sakatare na kungiyar ‘yan Lemo a kananan hukumomim Zariya da Sabon gari, ya ce, maid a hankalin ganin an kammala wannan hanya, shi ne zai sa al’ummar arewa za su ce sun amfana da mulkin da ake yi ma su daga shekara ta 2015 zuwannan shekara ta 2021 da a ke ciki.

SendShareTweetShare
Previous Post

Akwai Bara-gurbin Malamai Dake Wa ‘Yan Bindigar Addu’ar Samun Sa’a, Cewar Sakataren Gwamnatin Katsina

Next Post

2023: Ziyarar Gwamnonin APC Ga Jonathan Ba Barazana Ce Ga PDP Ba –Abubakar Baraje

RelatedPosts

IITA Ta Fara Horas Da Matasa Sana`o`in Dogaro Da Kai A Zariya

IITA Ta Fara Horas Da Matasa Sana`o`in Dogaro Da Kai A Zariya

by Sulaiman Ibrahim
2 days ago
0

Daga Nasiru Adamu Cibiyar kula da albarkatun aikin gona ta...

Garkuwa Da Dalibai: An Ceto Daliban Kagara, Ana Cigaba Da Neman Na Jangebe

Garkuwa Da Dalibai: An Ceto Daliban Kagara, Ana Cigaba Da Neman Na Jangebe

by Sulaiman Ibrahim
2 days ago
0

Daga Muhammad Awwal Umar, Minna Da sanyin safiyar asabar din...

Ma’aikatan Jinyar Jihar Ondo Za Su Fara Yajin Aikin Gargadi Na Kwana 3

Ma’aikatan Jinyar Jihar Ondo Za Su Fara Yajin Aikin Gargadi Na Kwana 3

by Sulaiman Ibrahim
2 days ago
0

Daga Idris Aliyu Daudawa kungiyar ma’aikatan jinya da unguwar-zoma ta...

Next Post
Jonathan

2023: Ziyarar Gwamnonin APC Ga Jonathan Ba Barazana Ce Ga PDP Ba –Abubakar Baraje

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version