• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Tsaurarra Dokar Hukunta Iyayen Da Ba Su Barin ‘Ya’yansu Mata Zuwa Boko

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
in Rahotonni
0
gaza
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Dattawa ta yi karatu na farko kan dokar da ta amince da cin tarar Naira 50,000 ga iyayen da suka ki sa ‘ya’yansu su samu ilimin makarantun Firamare da Sakandare,dokar da Sanatato Orji Kalu ya bukaci ayi mata gyara a sashi na (4) sakin layi na (b) na dokar inda aka goge Naira 2,000 inda aka maida Naira 20,000; sashe na (4) sakin layi na(c) inda aka sa Naira 5,000 aka sauya ta Naira 50,000 yayin da sashi na 3 sakin layi na (2) an sa dokar Naira 10,000 amma sai aka maida ta zuwa Naira 100,000.

Da yasa albarkacin bakin shi tsohon Shugaban majalisar dattawa ta kasa a majalisa ta tara Sanata Ahmed Lawan ya ce idan aka maida hankali akan ilmin ‘ya mace hakan zai bunkasa cigaban kasa sosai.
Lawan ya bayyana hakan ne ranar Laraba a wani bayani da mai ba shi shawara na harkokin yada labarai Ezrel Tabiowo ya raba wa manema labarai, saboda bikin ranar ilimin ‘ya mace na kasa da kasa.

  • Kashun Da Nijeriya Ke Fitarwa Ya Karu Daga Naira Biliyan 116 Zuwa 146.1
  • Za A Binciki Yadda Aka Karkatar Da Tallafin Korona Naira Biliyan 183.9

Kamar yadda ya ce, dan majalisar da yake wakiltar mazabar majalisar dattawa ta Yobe ta Arewa a majalisar dattawa ya kara jaddada cewa ilmantar da ‘ya mace samar da wata dama ce gare ta, ta yadda bada tata gudunmawar cigaban al’umma.

Shi ma Babban lauya na kasa Femi Falana cewa ya yi abu mafi dacewa shi ne majalisun kasar su tabbatar da yin dokar tsarin mulki da hakan zai ba Akanta Janar na kasa a kan ya cire daga asusun Jihohin zuwa gidauniyar kula da al’amuran ilimi.

Ga dai mganar da ya yi: “A tsarin da aka yi a na tunawa da ranar ‘ya mace ta kasa da kasa ta 2023 wadda aka yi ranar Alhamis, ‘yan majalisar wakilai ta kasa ba tare da wani bata lokaci ba suka amince da kudurin da suka cimmawa na sa ma’aikatar ilimi ta tarayya ta rage yawan yara ‘yan mata da basu zuwa makaranta, ta hanyar tabbatar da samar da ilimi kyauta kuma dole na ‘ya’ya mata a fadin tarayyar Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Ita ma ‘yar majalisar wakilai ta kasa Kafilat Ogbara (APC-Legas) da tace gidauniyar kasa da kasa kan al’amuran gaggawa na yara ta majalisar dinkin duniya UNICEF ta bayyana cewa akwai yara milyan 18.5 da basu zuwa makaranta inda kashi 60 ya nuna yara mata ne.Ta jaddada ‘yanmata suna da dama ta kasancewa ba wani abinda zai dame su,na da ilimi, da rayuwa mai cike da lafiya.

Honorabul Ogbara ta bayyana idan aka kul da rayuwar ‘yan mata sosai,ya kunshi samar da wani babin da zai ba ‘yanmata dama su rika bada gudunmawar su kan kowane tsarin da aka dauka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Karatun 'ya'ya mata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Aka Fara Cinikin Bayi (3)

Next Post

Maganin Ciwon Sanyi A Saukake

Related

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

19 hours ago
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

1 day ago
Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin
Rahotonni

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

2 days ago
Yadda Sanata Barau Ke Samar da Masana Don Ci Gaban Kano
Rahotonni

Yadda Sanata Barau Ke Samar da Masana Don Ci Gaban Kano

2 days ago
Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu
Rahotonni

Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu

1 week ago
Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba
Rahotonni

Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba

1 week ago
Next Post
Maganin Ciwon Sanyi A Saukake

Maganin Ciwon Sanyi A Saukake

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.