ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

by Bello Hamza
3 years ago
Peace

Shaharren Malamin addinin Musuluncin nan kuma shugaban kungiyar masu ilimin taurari na Afirka, Shekih Muhajjadina Sani kano na daya daga cikin fitattun manyan mutanen da kungiyar Arewa Peace Ambassador Forum ta karrama, inda aka nada shi a mastayin jakadan zaman lafiya a wani kasaitaccen taron da aka gudanar a a garin Kano, taron ya kuma yi daidai da bikin ranar zaman lafiya ta duniya wanda majalisar dinkin duniya ta kebe.

Inuwar jakadun zaman lafiya na Arewa”Arewa Peace Ambassador forum “ta gudanarda taron tunawa da ranar zaman lafiya ta Duniya a yammacin ranar Lahadi a birnin Kano.

  • Amurka Ita Ce “Daular Karya”Ta Ko Wace Fuska
  • Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kafa Sashi Na Musamman A NPA Don Inganta Ayyukanta

Kwamishinan ‘yan sanda na Jihar Kano wanda shima ya sani shaidar karramawa ta Ambasadan zaman lafiya, Muhammad Husaini Gumel shi ne ya shugabanci taron da ya sami halartar masana daban-daban suka gabatar da jawabai a kan taken taron da aka yi a kan cin zarafin jinsi.

ADVERTISEMENT

Ko’odinatan na kasa na inuwar jakadun zaman lafiya na Arewa jakadan Zaman lafiya, Nura Ali Abubakar ya shaida wa ‘yan jarida cewa makasudin gudanar da taron shi ne domin tunawa da ranar zaman lafiya ta Duniya saboda su jakadu ne na zaman lafiya duk abinda yake na inganta zaman lafiya ya kamata suma su taka muhimmiyar rawa akai.

Da ya daga cikin wadanda aka karrama da shaidar jakadan zaman lafiya a yayin taron Sheikh Muhajjanida Sani Kano, Shugaban kungiyar masu ilimin taurari na nahiyar Afirka kuma shugaban gidauniyar jinkai ta Muhajjadina Foundation, Maji dadin masarautar Yakalaje, ya ce gode wa Allah ya yi kuma farin ciki duba da yadda yan’uwa da iyaye da abokan arziki suka halarta domin nuna far in ciki gareshi na zama jakadan zaman lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

Ya kara da cewa wannan kuma ba abin mamaki ba ne domin duo abinda mutum yake na alkhairi al’umma na gani su ji dadi su yaba ba abin mamaki ba ne kaga wanda ka sani da wanda baka sani ba, da wanda baka zata ba su zo dan tayaka murna.

Ya ce wannan zai dada musu kwarin gwiwa cewa abin da suke al’umma na jin dadi suna farin ciki dan haka yana yi wa Allah godiya da suma al’ummar.

Sheikh Muhajjadina ya ce ita kanta kungiyar inuwar jakadun zaman lafiya ganin irin fadi tashi da suka na wayarwa jama’a kai da abubuwa da za su kawo musu zaman lafiya da suke yasa suka karramashi. Domin shi zaman lafiya ba abinda ya fishi suna rokon Allah ya baiwa kasarnan cikakkiyar zaman lafiya ya kara jaddada godiyarsa ga Allah da yadda jama’a suka taya shi murna.

Ambasada Sheik Muhajjadina ya yi kira ga dukkan al’ummar kasarnan a zauna lafiya musamnan matasa su zama masu inganta rayuwarsu da riko da gaskiya da amana da yin hakuri su guji shaye-shayen kwayoyi da zai sa su aikata abinda zai cutar da ci gaban rayuwarsu in suka zama masu tarbiyya za su samu gina lafiyayyiyar zuriya da za ta inganta al’umma.

Peace
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Next Post
Kasar Sin

Ofishin Jakadancin Kasar Sin Dake Najeriya Ya Shirya Bikin Murnar Cikar Sin Shekaru 74 Da Kafuwa

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.