• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Zargin Horo Da Ruwan Zafi Ya Jefa Rayuwar Budurwa Cikin Larura

by Rabi'u Ali Indabawa
11 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Jami’an Tsaro Sun Kashe Mahara 2, Sun Kwato Makamai A Anambra
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan uwan wata budurwa ‘yar shekara 23 mai suna Nana Fiddausi Sa’idu da ke da zama a Unguwar Makera gudunmar Rigasa a Karamar Hukumar Igabi a Jihar Kaduna, sun yi kira ga masu hannu da shuni, da su taimaka wa rayuwar buduwar, biyo bayan kamuwa da wata larura wanda hakan ya janyo halitta ta koma tamkar, ta karamar yarinya.

Wata kanwar mahaifiyarta mai suna A’i ta yi zargin cewa, Nana ta kamu da larurar ce, bayan da mahaifin Nana ya dauke ta daga gun dangin mahaifiyar ta ya kuma ya mayar da ita ga wata ‘yaruwarsa da ke a Jihar Kano.

  • Kashi 67 Cikin 100 Na Ɗaliban Kaduna Sun Samu Nasara A WAEC – Kwamishinan Ilimi
  • Ronaldo Da Messi Ne Kan Gaba A Jerin ‘Yan Wasan Da Suka Fi Karbar Albashi

Ta ce, lafiyar ta lau mahaifinta ya dauke ta daga wurinsu amma sai ta gudo daga gun ‘yaruwar ta sa daga Kano saboda ‘yar uwar uban, na yi mata mata horo da ruwan zafi.

A cewarta, Nana ta je tashar mota ta Kano ne, inda ta nemi taimakon mutane da su sanya a mota ta dawo Kadauna, suka dauko ta suka kawo ta gidanmu.

Ta ce, bayan da Nana ta kamu da larurar babu wata kulawa daga mahaifinta, ya yi wasti da ita, kuma ‘yanu wansa babu wanda ya damu da halin da take a ciki.

Labarai Masu Nasaba

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

Ta ce, bayan kwana biyu ta fadi aka kaita asibitin Nasiha ba a cikin hayyacinta ba, aka kwantar da ita, a rika kiran mahaifinta a waya, daga baya ya zo ya iske, ana yi mata karin ruwa, sai ya cire robar karin ruwan har suka fara sa-insa da wata jami’ar asibitin, amma ya matsa sai da aka cire mata aka dawo da ita gida.

Ai ta ce, larurar ta koma mata kamar farfadiya, wanda duk inda take, sai ta fadi tana fisge-fisge, yanzu gashi mahaifinta ya rasu, kuma ‘yanuwansa, babu wanda ya damu da halin laruwar da take ciki.

Da aka tambaye ta ko sun sanar da hukuma lamarin ta ce, ba a sanar da hukuma ba, inda ta ce, tun ana yi mata magani, yanzu dai karfinsu ya kare, amma suna neman taimako don a ceto raywarta.

Shi ma Ibrahim Hannafi wanda yayan mahaifiyar Nana ne, ya zargi ‘yan uwan mahaifi da nuna halin ko in kula a kan larurar Nana, inda ya yi kira ga masu hali, da su taimaka a ceto raywar budurwar.

Ya ce, lokacin mahaifinsu yana raye, shi ne yake kulawa da halin da take ciki amma ya ce, mu kyale, ‘yan uwan mahaifinta da halin sun nuna ko in kula dangane da larurar ta, kuma bai bar su mun dauki wani mataki ba a lokacin da yake raye.

Shi kuwa Malam Anas Musa dan kungiyar kare hakkin ‘yan’Adam cewa ya yi, an zalunci yarinyar, duba da yadda dangin mahaifinta suka yi watsi da ita, suka bar nauyinta a gun dangin uwarta, inda ya ce, a kungiyance, za mu bi wa Nana kadin tauye mata ‘yancinta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BudurwaHoro
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Kama Wata Mata Da Laifin Azabtar Da Yara Kanana A Adamawa

Next Post

Kotu Ta Garkame Wani Dan Shekara 43 Da Ya Lalata Agolarsa

Related

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

3 weeks ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

3 weeks ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

3 weeks ago
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

4 weeks ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

4 weeks ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

4 weeks ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Tsohowar Shugaban Kotun Gargajiya A Benue

Kotu Ta Garkame Wani Dan Shekara 43 Da Ya Lalata Agolarsa

LABARAI MASU NASABA

Ahlul Faidhati Mai Diwani Group

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

September 12, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

September 12, 2025
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

September 12, 2025
Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

September 12, 2025
Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

September 12, 2025
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

September 12, 2025
Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

September 12, 2025
Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

September 12, 2025
Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

September 12, 2025
Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.