ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaje-Yajen Aiki Na Neman Yi Wa Gwamnatin Buhari Katutu 

by Sabo Ahmad and Idris Aliyu Daudawa
4 years ago
Buhari

Yajin aiki wata hanya ce da ma’aikata ke bi domin ganin an biya su hakkokinsu na aiki. Yajin aiki a Nijeriya na neman kasa samun tasiri wajen gwamnati.

Yanzu haka malaman jami’a sun kwashe watanni suna daka yajin amma, har yanzu kwalliya ta kasa biyan kudin sabulu.

  • Buhari Ya Mika Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Tsohon Sufeton ‘Yansanda Tafa Balogun
  • Jihar Nasarawa Ta Fadakar Da Al’ummarta A Kan Cutar Hanta

A karshen watan da ya gabata ne shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bayar wa’adin mako biyu ga masu ruwa da tsaki kan harkar ilimi da su tabbatar da warware wannan matsala cikin mako biyu, amma sai ga shi har zuwa wannan lokaci, ba a cika wannan umarni na shugaban kasa ba, al’amarin da ya sa ASUU ta ba da sabon umarni na ci gaba da yajin aikin, al’amarin da zai kara jefa daliban da ke zaune a gida, halin damuwa.

ADVERTISEMENT

Sai dai duk da ci gaba da wannan yajin aikin yanzu haka, ana ci gaba da tattauna wa da gwamnati kan wannan lamari, sai dai abin tambayar shi ne, yaushe za a cim ma matsaya, wannan shi ne abin da ‘yan Nijeriya suka matsu su ji, domin kuwa, an dade ana tafka ruwa kasa tana shanye wa.

Don haka ne ma malaman jami’ar suka ja daga a wannan karon, da niyyar sai sun ga abin da ya ture wa buzu nadi.

LABARAI MASU NASABA

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto

Shi dai yajin aiki wata hanya ce da ma’aikata ke bi, wajen ta kaurace wa zuwa gurin da suke yin aiki, da niyyar sai biya musu bukatunsu kafin su koma.

Wani lokaci hakarsu na cim ma ruwa, wani lokacin kuma haka nan za su gaji su koma bakin aikin ba tare da samun biyan bukatar ba.

Zuwa yanzu yajin aikin da kungiyar malaman jami’oi ta kasa ta shiga koda yake ba shi ba ne na farko, na wanann shekarar dai an fara shi ne ranar 14 ga watan Fabarairu na shekara ta 2022, wanda kungiyar ta bukaci a biya mata bukatunta da suka yi yarjejeniya da gwamnatin tarayya, amma ba a samu cika mata su ba.

Yau kwana 172 ke nan, watau fiye da wata biyar ke nan daliban jam’o’i suke zaune a gida ba tare.

Ranar Lahadi 31 ga watan Yuni 2022 ta makon da ya wuce ne wa’adinta na mako hudu ya cika, ba tare da samun cimma buri ba,hakan shi ya sa, ASUU ta sake ba da wani wa’adin na wasu karin mako hudu.

Idan dai ba a manta ba, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ba Ministan ilimi Adamu Adamu mako biyu da ya kawo karshen yajin aikin.

Sai dai bisa ga dukkan alamu ba a samu cim ma wata matsaya ba, shi ya sa suka kara bada wani wa’adin mako hudu wanda ya fara daga 1 ga watan Agusta 2022.

Kungiyar ASUU ba ita kadai ba ce a gwagwarmayar da take yi ta ganin an koma bakin aiki ba bayan biya mata bukatunta, domin kuwa kungiyar kwadago ta kasa NLC na daga cikin masu mara ma ta baya, inda ta shiga kwarya-kwaryar zanga- zanga ta kasa baki daya ta kwana biyu, domin nuna goyon bayan a biya mata hakkinta a ranar 26 da 27 ga watan Yuli 2022.

Wasu kungiyoyi da dama su ma ba a bar su a baya ba, domin kuwa sun goya ma ita kungiyar baya ta ganin an biya mata hakkinta.

Ba kungiyar ASUU kadai ta shiga yajin aiki ba domin kuwa kungiyar manyan ma’aikata jami’o’i ta kasa SSANU suna mara musu baya.

Abin bai tsaya a nan ba, saboda kungiyar Likitoci masu koyon aiki “Resident Doctors Association” wadda ita ma ba wannan ba ne karo na farko da fara shiga irin yajin aiki ba domin wa’adi ne ta bayar.Ita ma ta bada wa’adin mako biyu ma gwamnatin tarayya ta biya mata bukatunta ko kuma ta tsunduma cikin yajin aiki, kamar ASUU ta saba shiga irin wannan yajin aikin, ta tafi ta bar marasa lafiya wasu kwance a asbiti ba tare da cikakkiyar kulawa ba, wasu suna mutuwa, wasu su kara tagaiyara ba masu kulawa da lafiyarsu,ba tare da samun an biya mata dukkan bukatun nata ba.

Buhari
Sabo Ahmad
+ posts Bio
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    An Gurfanar Da Mutum 3 Bisa Laifin Lakada Wa Wani Duka Har Lahira
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Dalilin Da Ya Sa Kotu Ta Tasa Keyar Dakta Idris Dutsen Tanshi Zuwa Gidan Yari
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Uwa Ta Mutu A Kokarin Raba Fada Tsakanin ‘Ya’yanta A Abuja
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    ’Yan Fashi Sun Yi Shigar Injiniyoyi, Sun Saci Manyan Na’urorin Sadarwa
Buhari
Idris Aliyu Daudawa
+ posts Bio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

MASU ALAKA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Rahotonni

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

July 25, 2026
Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe
Rahotonni

Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto

July 25, 2026
NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci
Rahotonni

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026
Next Post
Masana Sun Bukaci Mata Masu Aiki Su Rungumi Akidar Shayar Da Jariransu Nonon Uwa

Masana Sun Bukaci Mata Masu Aiki Su Rungumi Akidar Shayar Da Jariransu Nonon Uwa

LABARAI MASU NASABA

Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

July 27, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

July 27, 2026
Buhari

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

July 27, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

July 27, 2026
Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
Buhari

WAFU B 2026: Nijeriya Ta Doke Ghana Da Ci 4-2 A Wasan Farko

July 27, 2026
An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

July 27, 2026
Buhari

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026
Buhari

Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu

July 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.