ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaje-Yajen Aiki Na Neman Yi Wa Gwamnatin Buhari Katutu 

by Sabo Ahmad and Idris Aliyu Daudawa
4 years ago
Buhari

Yajin aiki wata hanya ce da ma’aikata ke bi domin ganin an biya su hakkokinsu na aiki. Yajin aiki a Nijeriya na neman kasa samun tasiri wajen gwamnati.

Yanzu haka malaman jami’a sun kwashe watanni suna daka yajin amma, har yanzu kwalliya ta kasa biyan kudin sabulu.

  • Buhari Ya Mika Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Tsohon Sufeton ‘Yansanda Tafa Balogun
  • Jihar Nasarawa Ta Fadakar Da Al’ummarta A Kan Cutar Hanta

A karshen watan da ya gabata ne shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bayar wa’adin mako biyu ga masu ruwa da tsaki kan harkar ilimi da su tabbatar da warware wannan matsala cikin mako biyu, amma sai ga shi har zuwa wannan lokaci, ba a cika wannan umarni na shugaban kasa ba, al’amarin da ya sa ASUU ta ba da sabon umarni na ci gaba da yajin aikin, al’amarin da zai kara jefa daliban da ke zaune a gida, halin damuwa.

ADVERTISEMENT

Sai dai duk da ci gaba da wannan yajin aikin yanzu haka, ana ci gaba da tattauna wa da gwamnati kan wannan lamari, sai dai abin tambayar shi ne, yaushe za a cim ma matsaya, wannan shi ne abin da ‘yan Nijeriya suka matsu su ji, domin kuwa, an dade ana tafka ruwa kasa tana shanye wa.

Don haka ne ma malaman jami’ar suka ja daga a wannan karon, da niyyar sai sun ga abin da ya ture wa buzu nadi.

LABARAI MASU NASABA

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

Shi dai yajin aiki wata hanya ce da ma’aikata ke bi, wajen ta kaurace wa zuwa gurin da suke yin aiki, da niyyar sai biya musu bukatunsu kafin su koma.

Wani lokaci hakarsu na cim ma ruwa, wani lokacin kuma haka nan za su gaji su koma bakin aikin ba tare da samun biyan bukatar ba.

Zuwa yanzu yajin aikin da kungiyar malaman jami’oi ta kasa ta shiga koda yake ba shi ba ne na farko, na wanann shekarar dai an fara shi ne ranar 14 ga watan Fabarairu na shekara ta 2022, wanda kungiyar ta bukaci a biya mata bukatunta da suka yi yarjejeniya da gwamnatin tarayya, amma ba a samu cika mata su ba.

Yau kwana 172 ke nan, watau fiye da wata biyar ke nan daliban jam’o’i suke zaune a gida ba tare.

Ranar Lahadi 31 ga watan Yuni 2022 ta makon da ya wuce ne wa’adinta na mako hudu ya cika, ba tare da samun cimma buri ba,hakan shi ya sa, ASUU ta sake ba da wani wa’adin na wasu karin mako hudu.

Idan dai ba a manta ba, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ba Ministan ilimi Adamu Adamu mako biyu da ya kawo karshen yajin aikin.

Sai dai bisa ga dukkan alamu ba a samu cim ma wata matsaya ba, shi ya sa suka kara bada wani wa’adin mako hudu wanda ya fara daga 1 ga watan Agusta 2022.

Kungiyar ASUU ba ita kadai ba ce a gwagwarmayar da take yi ta ganin an koma bakin aiki ba bayan biya mata bukatunta, domin kuwa kungiyar kwadago ta kasa NLC na daga cikin masu mara ma ta baya, inda ta shiga kwarya-kwaryar zanga- zanga ta kasa baki daya ta kwana biyu, domin nuna goyon bayan a biya mata hakkinta a ranar 26 da 27 ga watan Yuli 2022.

Wasu kungiyoyi da dama su ma ba a bar su a baya ba, domin kuwa sun goya ma ita kungiyar baya ta ganin an biya mata hakkinta.

Ba kungiyar ASUU kadai ta shiga yajin aiki ba domin kuwa kungiyar manyan ma’aikata jami’o’i ta kasa SSANU suna mara musu baya.

Abin bai tsaya a nan ba, saboda kungiyar Likitoci masu koyon aiki “Resident Doctors Association” wadda ita ma ba wannan ba ne karo na farko da fara shiga irin yajin aiki ba domin wa’adi ne ta bayar.Ita ma ta bada wa’adin mako biyu ma gwamnatin tarayya ta biya mata bukatunta ko kuma ta tsunduma cikin yajin aiki, kamar ASUU ta saba shiga irin wannan yajin aikin, ta tafi ta bar marasa lafiya wasu kwance a asbiti ba tare da cikakkiyar kulawa ba, wasu suna mutuwa, wasu su kara tagaiyara ba masu kulawa da lafiyarsu,ba tare da samun an biya mata dukkan bukatun nata ba.

Buhari
Sabo Ahmad
+ posts Bio
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    An Gurfanar Da Mutum 3 Bisa Laifin Lakada Wa Wani Duka Har Lahira
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Dalilin Da Ya Sa Kotu Ta Tasa Keyar Dakta Idris Dutsen Tanshi Zuwa Gidan Yari
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Uwa Ta Mutu A Kokarin Raba Fada Tsakanin ‘Ya’yanta A Abuja
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    ’Yan Fashi Sun Yi Shigar Injiniyoyi, Sun Saci Manyan Na’urorin Sadarwa
Buhari
Idris Aliyu Daudawa
+ posts Bio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Rayuwar Galadiman Kano Alhaji Tijjani Hashim (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kyamar Baƙi: An Sake Kwaso Ƴan Nijeriya 83 Daga Afirka Ta Kudu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 60 Da Kayan Aiki A Edo
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tsohon Shugaban Ƙasa Jonathan Ya Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Ƙasa 18 A Jihar Bauchi

MASU ALAKA

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Umarnin Kawo Karshen Matsalar Tsaro
Rahotonni

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

September 5, 2026
Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
Rahotonni

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

September 5, 2026
Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
Rahotonni

Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki

September 5, 2026
Next Post
Masana Sun Bukaci Mata Masu Aiki Su Rungumi Akidar Shayar Da Jariransu Nonon Uwa

Masana Sun Bukaci Mata Masu Aiki Su Rungumi Akidar Shayar Da Jariransu Nonon Uwa

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.