ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaje-Yajen Aiki Na Neman Yi Wa Gwamnatin Buhari Katutu 

by Sabo Ahmad and Idris Aliyu Daudawa
4 years ago
Buhari

Yajin aiki wata hanya ce da ma’aikata ke bi domin ganin an biya su hakkokinsu na aiki. Yajin aiki a Nijeriya na neman kasa samun tasiri wajen gwamnati.

Yanzu haka malaman jami’a sun kwashe watanni suna daka yajin amma, har yanzu kwalliya ta kasa biyan kudin sabulu.

  • Buhari Ya Mika Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Tsohon Sufeton ‘Yansanda Tafa Balogun
  • Jihar Nasarawa Ta Fadakar Da Al’ummarta A Kan Cutar Hanta

A karshen watan da ya gabata ne shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bayar wa’adin mako biyu ga masu ruwa da tsaki kan harkar ilimi da su tabbatar da warware wannan matsala cikin mako biyu, amma sai ga shi har zuwa wannan lokaci, ba a cika wannan umarni na shugaban kasa ba, al’amarin da ya sa ASUU ta ba da sabon umarni na ci gaba da yajin aikin, al’amarin da zai kara jefa daliban da ke zaune a gida, halin damuwa.

ADVERTISEMENT

Sai dai duk da ci gaba da wannan yajin aikin yanzu haka, ana ci gaba da tattauna wa da gwamnati kan wannan lamari, sai dai abin tambayar shi ne, yaushe za a cim ma matsaya, wannan shi ne abin da ‘yan Nijeriya suka matsu su ji, domin kuwa, an dade ana tafka ruwa kasa tana shanye wa.

Don haka ne ma malaman jami’ar suka ja daga a wannan karon, da niyyar sai sun ga abin da ya ture wa buzu nadi.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

Shi dai yajin aiki wata hanya ce da ma’aikata ke bi, wajen ta kaurace wa zuwa gurin da suke yin aiki, da niyyar sai biya musu bukatunsu kafin su koma.

Wani lokaci hakarsu na cim ma ruwa, wani lokacin kuma haka nan za su gaji su koma bakin aikin ba tare da samun biyan bukatar ba.

Zuwa yanzu yajin aikin da kungiyar malaman jami’oi ta kasa ta shiga koda yake ba shi ba ne na farko, na wanann shekarar dai an fara shi ne ranar 14 ga watan Fabarairu na shekara ta 2022, wanda kungiyar ta bukaci a biya mata bukatunta da suka yi yarjejeniya da gwamnatin tarayya, amma ba a samu cika mata su ba.

Yau kwana 172 ke nan, watau fiye da wata biyar ke nan daliban jam’o’i suke zaune a gida ba tare.

Ranar Lahadi 31 ga watan Yuni 2022 ta makon da ya wuce ne wa’adinta na mako hudu ya cika, ba tare da samun cimma buri ba,hakan shi ya sa, ASUU ta sake ba da wani wa’adin na wasu karin mako hudu.

Idan dai ba a manta ba, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ba Ministan ilimi Adamu Adamu mako biyu da ya kawo karshen yajin aikin.

Sai dai bisa ga dukkan alamu ba a samu cim ma wata matsaya ba, shi ya sa suka kara bada wani wa’adin mako hudu wanda ya fara daga 1 ga watan Agusta 2022.

Kungiyar ASUU ba ita kadai ba ce a gwagwarmayar da take yi ta ganin an koma bakin aiki ba bayan biya mata bukatunta, domin kuwa kungiyar kwadago ta kasa NLC na daga cikin masu mara ma ta baya, inda ta shiga kwarya-kwaryar zanga- zanga ta kasa baki daya ta kwana biyu, domin nuna goyon bayan a biya mata hakkinta a ranar 26 da 27 ga watan Yuli 2022.

Wasu kungiyoyi da dama su ma ba a bar su a baya ba, domin kuwa sun goya ma ita kungiyar baya ta ganin an biya mata hakkinta.

Ba kungiyar ASUU kadai ta shiga yajin aiki ba domin kuwa kungiyar manyan ma’aikata jami’o’i ta kasa SSANU suna mara musu baya.

Abin bai tsaya a nan ba, saboda kungiyar Likitoci masu koyon aiki “Resident Doctors Association” wadda ita ma ba wannan ba ne karo na farko da fara shiga irin yajin aiki ba domin wa’adi ne ta bayar.Ita ma ta bada wa’adin mako biyu ma gwamnatin tarayya ta biya mata bukatunta ko kuma ta tsunduma cikin yajin aiki, kamar ASUU ta saba shiga irin wannan yajin aikin, ta tafi ta bar marasa lafiya wasu kwance a asbiti ba tare da cikakkiyar kulawa ba, wasu suna mutuwa, wasu su kara tagaiyara ba masu kulawa da lafiyarsu,ba tare da samun an biya mata dukkan bukatun nata ba.

Buhari
Sabo Ahmad
+ posts Bio
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    An Gurfanar Da Mutum 3 Bisa Laifin Lakada Wa Wani Duka Har Lahira
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Dalilin Da Ya Sa Kotu Ta Tasa Keyar Dakta Idris Dutsen Tanshi Zuwa Gidan Yari
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Uwa Ta Mutu A Kokarin Raba Fada Tsakanin ‘Ya’yanta A Abuja
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    ’Yan Fashi Sun Yi Shigar Injiniyoyi, Sun Saci Manyan Na’urorin Sadarwa
Buhari
Idris Aliyu Daudawa
+ posts Bio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

MASU ALAKA

Buhari
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Buhari
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Masana Sun Bukaci Mata Masu Aiki Su Rungumi Akidar Shayar Da Jariransu Nonon Uwa

Masana Sun Bukaci Mata Masu Aiki Su Rungumi Akidar Shayar Da Jariransu Nonon Uwa

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.