• English
  • Business News
Saturday, May 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

by Yusuf Shuaibu
4 hours ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Manyan jam’iyyun adawa a kasar nan na ci gaba da caccakar shugabannin jam’iyyar APC saboda goyon bayan tazarcen Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu kan damar samun wa’adin mulki na biyu.

Rahotanni na cewa manyan jiga-jigan APC sun yi amfani da duk hanyoyin da suke da su domin yaba wa gwamnatin Tinubu da kuma goyon bayan sa don sake tsayawa takara a 2027.

  • Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ke Iya Samar Ta Amfani Da Karfin Ruwa Ta Kai Matsayin Koli A Duniya
  • Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur

A lokacin da shugabannin APC a Arewa Maso Yamma suka goyi bayan shugaban kasar a karshen mako a Kaduna, jam’iyyun adawa sun nuna rashin jin dadinsu game da wannan lamari.

Shugaban APC na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje da gwamnonin da ke cikin jam’iyyar daga yanki, ciki har da Uba Sani na Jihar Kaduna, Nasir Idris na Kebbi, da Umar Namadi na Jigawa sun halarci taron.

Sauran sun hada da shugaban majalisar wakilai, Dakta Tajudeen Abbas da mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau I Jibrin, ministocin daga yanki, shugabannin kananan hukumomin APC, masu wakiltar jihohi da na kasa tare da shugabannin hukumomin tarayya.

Labarai Masu Nasaba

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

An dai fara goyon bayan tazarcen Tinubu a wurin taron lokacin da mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau Jibrin, ya ce babu wani gurbi a fadar shugaban kasa a 2027.

Barau ya ce, “A bayyane yake a 2027, za mu sami gagarumar nasara, In Sha Allah. Don haka, mu ci gaba da hanyar da muke kai. Mu hada kai da juna, mu yi aiki tare da shugaban kasa, mu yi aiki tare da kowa, mu hada kai a tsakaninmu don samun nasarar da ake bukata.”

Sanata Barau ya ci gaba da cewa sauya shekan wasu shugabannin jam’iyyun adawa zuwa APC ya kasance sakamakon aikin Shugaba Tinubu a cikin shekaru biyu kawai da ya shafe a kan karagar mulkin Nijeriya.

Kazalika, Ganduje ya ce Shugaba Tinubu na da kishin ci gaban Arewa Maso Yamma da dukkan yankin Arewa da ma Nijeriya gaba daya, don haka ya cancanci wa’adin mulki na biyu.

Ya ce yi matukar yin kokari ta hanyar wasu ayyukan da gwamnatisa ta bijiro da su, tun daga kan samar da kayayyakin more rayuwa har zuwa bunkasa bangaren noma a yankin Arewa.

Ganduje ya jaddada cewa kafa ma’aikatar bunkasa yankin Arewa Maso Yamma alama ce a fili na cewa shugaban kasa yana son yankin Arewa Maso Yamma.

Haka kuma, Gwamna Uba Sani ya ce yankin Arewaci Maso Yammaci ya bunkasa a karkashin jagorancin Shugaban kasa Tinubu.

“Shugaba Tinubu ya karbi iko ne lokacin da al’amuran kasarmu suka kasance mafi munin kalubale a tarihinta,” in ji shi.

Ya yaba da canje-canje masu amfani na Tinubu, yana cewa, “Shugaban ba ya jin tsoron yanke shawara masu wahala. ‘Yan Nijeriya ma sun fara fahimtar cewa Mai Girma Shugaba yana da kyawawan manufofi ga kasarmu.”

A nasa jawabin, shugaban majalisar wakilai, Abbas Tajudeen, ya ce ficewar wasu daga jam’iyyun adawa zuwa APC ya nuna karuwar yarda da ‘yan Nijeriya ke nuna wa jam’iyyar da shugabancinta, amma ya jaddada cewa jam’iyyar dole ne ta karfafa yawan masu goyon baya tun daga mataki na kasa.

A cikin martaninsa, shugaban jam’iyyar ADC, Dakta Ralphs Okey Nwosu, ya ce Tinubu bai cancanci yin tazarce ba.

Nwosu, a wata tattaunawa ta wayar tarho da manema labarai, ya ce idan aka duba matsayin shugaban kasa bisa kashi, yana iya samun kashi 10 kacal cikin dari sakamakon rashin tsinana abun kirki na shugabancin kasar nan.

Da yake magana kan goyon bayan shugaban kasa daga masu ruwa da tsaki na APC a Kaduna, Nwosu ya ce ‘yan adawa ne kadai za su iya ceto kasar nan, yana mai cewa idan har APC ta ci gaba da mulki a 2027, mutane da yawa daga cikin ‘yan Nijeriya za su mutu da yunwa.

Amma jam’iyyar SDP ta ce ‘yan Nijeriya za su tantance wane ne zai yi nasara a zaben shugaban kasa na 2027 idan lokaci ya yi.

Sakataren yada labarai na jam’iyyar, Araba Rufus Aiyenigba, ya shaida hakan, inda ya ce, “Mutanen Nijeriya ne za su tantance wanda zai zama shugaban kasan Nijeriya a 2027, ba shugabannin APC ba,” in ji Aiyenigba.

Sakataren yada labarai na NNPP, Ladipo Johnson, ya ce goyon baya daga cikin gida na jam’iyya na da karancin tasiri wajen gwada gwazon gwamnati.

Shi kuwa wani mamba na kwamitin zartarwa na jam’iyyar PDP, Tim Osadolor ya ce goyon bayan Shugaba Tinubu ba zai haifar da komai ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Tinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Kasar Sin Ya Jaddada Muhimmancin Samun Ci Gaba Mai Inganci Ta Fuskar Raya Wayewar Kai

Next Post

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz

Related

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

3 hours ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

3 weeks ago
Tinubu
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

3 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

3 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

4 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

4 weeks ago
Next Post
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Bukaci Kada Amurka Ta Siyasantar Da Hadin Gwiwar Bangaren Ilimi

Sin Ta Bukaci Kada Amurka Ta Siyasantar Da Hadin Gwiwar Bangaren Ilimi

May 23, 2025
Kamfanoni Masu Jarin Waje Sun Ci Gajiyar Tsarin Kasar Sin Na Samar Da Rangwamen Gwamnati Ta Musayar Sabbin Kayayyaki Da Tsofaffi

Kamfanoni Masu Jarin Waje Sun Ci Gajiyar Tsarin Kasar Sin Na Samar Da Rangwamen Gwamnati Ta Musayar Sabbin Kayayyaki Da Tsofaffi

May 23, 2025
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

May 23, 2025
Sin Da ASEAN Sun Kammala Tattaunawa Game Da Kafa Yankin Ciniki Cikin ‘Yanci

Sin Da ASEAN Sun Kammala Tattaunawa Game Da Kafa Yankin Ciniki Cikin ‘Yanci

May 23, 2025
An Gudanar Da Taron Kolin Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Na Duniya Na Shekara Ta 2025 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kolin Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Na Duniya Na Shekara Ta 2025 A Beijing

May 23, 2025
Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

May 23, 2025
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

May 23, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz

May 23, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

May 23, 2025
Shugaban Kasar Sin Ya Jaddada Muhimmancin Samun Ci Gaba Mai Inganci Ta Fuskar Raya Wayewar Kai

Shugaban Kasar Sin Ya Jaddada Muhimmancin Samun Ci Gaba Mai Inganci Ta Fuskar Raya Wayewar Kai

May 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.