• English
  • Business News
Thursday, July 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

by Yusuf Shuaibu
1 month ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Manyan jam’iyyun adawa a kasar nan na ci gaba da caccakar shugabannin jam’iyyar APC saboda goyon bayan tazarcen Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu kan damar samun wa’adin mulki na biyu.

Rahotanni na cewa manyan jiga-jigan APC sun yi amfani da duk hanyoyin da suke da su domin yaba wa gwamnatin Tinubu da kuma goyon bayan sa don sake tsayawa takara a 2027.

  • Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ke Iya Samar Ta Amfani Da Karfin Ruwa Ta Kai Matsayin Koli A Duniya
  • Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur

A lokacin da shugabannin APC a Arewa Maso Yamma suka goyi bayan shugaban kasar a karshen mako a Kaduna, jam’iyyun adawa sun nuna rashin jin dadinsu game da wannan lamari.

Shugaban APC na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje da gwamnonin da ke cikin jam’iyyar daga yanki, ciki har da Uba Sani na Jihar Kaduna, Nasir Idris na Kebbi, da Umar Namadi na Jigawa sun halarci taron.

Sauran sun hada da shugaban majalisar wakilai, Dakta Tajudeen Abbas da mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau I Jibrin, ministocin daga yanki, shugabannin kananan hukumomin APC, masu wakiltar jihohi da na kasa tare da shugabannin hukumomin tarayya.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

An dai fara goyon bayan tazarcen Tinubu a wurin taron lokacin da mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau Jibrin, ya ce babu wani gurbi a fadar shugaban kasa a 2027.

Barau ya ce, “A bayyane yake a 2027, za mu sami gagarumar nasara, In Sha Allah. Don haka, mu ci gaba da hanyar da muke kai. Mu hada kai da juna, mu yi aiki tare da shugaban kasa, mu yi aiki tare da kowa, mu hada kai a tsakaninmu don samun nasarar da ake bukata.”

Sanata Barau ya ci gaba da cewa sauya shekan wasu shugabannin jam’iyyun adawa zuwa APC ya kasance sakamakon aikin Shugaba Tinubu a cikin shekaru biyu kawai da ya shafe a kan karagar mulkin Nijeriya.

Kazalika, Ganduje ya ce Shugaba Tinubu na da kishin ci gaban Arewa Maso Yamma da dukkan yankin Arewa da ma Nijeriya gaba daya, don haka ya cancanci wa’adin mulki na biyu.

Ya ce yi matukar yin kokari ta hanyar wasu ayyukan da gwamnatisa ta bijiro da su, tun daga kan samar da kayayyakin more rayuwa har zuwa bunkasa bangaren noma a yankin Arewa.

Ganduje ya jaddada cewa kafa ma’aikatar bunkasa yankin Arewa Maso Yamma alama ce a fili na cewa shugaban kasa yana son yankin Arewa Maso Yamma.

Haka kuma, Gwamna Uba Sani ya ce yankin Arewaci Maso Yammaci ya bunkasa a karkashin jagorancin Shugaban kasa Tinubu.

“Shugaba Tinubu ya karbi iko ne lokacin da al’amuran kasarmu suka kasance mafi munin kalubale a tarihinta,” in ji shi.

Ya yaba da canje-canje masu amfani na Tinubu, yana cewa, “Shugaban ba ya jin tsoron yanke shawara masu wahala. ‘Yan Nijeriya ma sun fara fahimtar cewa Mai Girma Shugaba yana da kyawawan manufofi ga kasarmu.”

A nasa jawabin, shugaban majalisar wakilai, Abbas Tajudeen, ya ce ficewar wasu daga jam’iyyun adawa zuwa APC ya nuna karuwar yarda da ‘yan Nijeriya ke nuna wa jam’iyyar da shugabancinta, amma ya jaddada cewa jam’iyyar dole ne ta karfafa yawan masu goyon baya tun daga mataki na kasa.

A cikin martaninsa, shugaban jam’iyyar ADC, Dakta Ralphs Okey Nwosu, ya ce Tinubu bai cancanci yin tazarce ba.

Nwosu, a wata tattaunawa ta wayar tarho da manema labarai, ya ce idan aka duba matsayin shugaban kasa bisa kashi, yana iya samun kashi 10 kacal cikin dari sakamakon rashin tsinana abun kirki na shugabancin kasar nan.

Da yake magana kan goyon bayan shugaban kasa daga masu ruwa da tsaki na APC a Kaduna, Nwosu ya ce ‘yan adawa ne kadai za su iya ceto kasar nan, yana mai cewa idan har APC ta ci gaba da mulki a 2027, mutane da yawa daga cikin ‘yan Nijeriya za su mutu da yunwa.

Amma jam’iyyar SDP ta ce ‘yan Nijeriya za su tantance wane ne zai yi nasara a zaben shugaban kasa na 2027 idan lokaci ya yi.

Sakataren yada labarai na jam’iyyar, Araba Rufus Aiyenigba, ya shaida hakan, inda ya ce, “Mutanen Nijeriya ne za su tantance wanda zai zama shugaban kasan Nijeriya a 2027, ba shugabannin APC ba,” in ji Aiyenigba.

Sakataren yada labarai na NNPP, Ladipo Johnson, ya ce goyon baya daga cikin gida na jam’iyya na da karancin tasiri wajen gwada gwazon gwamnati.

Shi kuwa wani mamba na kwamitin zartarwa na jam’iyyar PDP, Tim Osadolor ya ce goyon bayan Shugaba Tinubu ba zai haifar da komai ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Tinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Kasar Sin Ya Jaddada Muhimmancin Samun Ci Gaba Mai Inganci Ta Fuskar Raya Wayewar Kai

Next Post

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

3 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

3 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

4 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 month ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

2 months ago
Next Post
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Ceto Ɗan Ghana, Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 3

July 3, 2025
Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu

Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu

July 3, 2025
Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

July 2, 2025
Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

July 2, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

July 2, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

July 2, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

July 2, 2025
Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

July 2, 2025
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

July 2, 2025
Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

July 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.