• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa Ayarin Yahaya Bello Hari, Sun Raunata Jami’an Tsaro

by Sadiq
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
‘Yan Bindiga Sun Kai Wa Ayarin Yahaya Bello Hari, Sun Raunata Jami’an Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Kogi ta ce wasu ‘yan bindiga sun kai wa ayarin motocin Gwamna Yahaya Bello hari a kan hanyar Abuja zuwa Lokoja.

Ta ce an kai harin ne a kusa da wani sansanin sojin ruwa, mai tazarar kilomita kadan daga Lokoja, babban birnin jihar.

  • Wane Ne Sabon Kocin Chelsea Mauricio Po-chettino?
  • Gwamnan Bauchi Ya Zama Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP

Kwamishinan yada labaran Jihar Kogi, Kingsley Fanwo ne, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Lokoja.

Fanwo ya yi zargin cewa ‘yan bindigar ‘yan barandan siyasa ne na wata jam’iyyar adawa ta SDP a jihar.

Kwamishinan ya ce lamarin da ya faru da misalin karfe 12:30 na rana, ya yi sanadin jikkatar mutane da dama da suka hada da jami’an tsaro wanda aka kai su asibiti domin kula da lafiyarsu.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

“’Yan bindigar da ake zargin ‘yan bangar siyasa ne na jam’iyyar SDP, da suka hango ayarin Bello suna tahowa, sai suka tare hanya suka fara harbinsu.

“Amma Alhamdulillahi gwamnanmu ya tsira ba tare da samun wani rauni ba.

“Wasu mataimakan tsaro da sauran masu taimaka wa gwamnan sun samu raunuka, kuma an garzaya da su asibiti domin kula da su.

“Muna kira ga jama’ar Kogi da su kwantar da hankalinsu domin jami’an tsaro suna bincike dk cafke ‘yan bindigar da suka kai harin,” in ji shi.

Fanwo ya ce gwamnatin jihar ba za ta amince da karya doka da oda ba amma za ta yi duk mai yiwuwa domin gurfanar da maharan a gaban kuliya.

A cewarsa, gwamnan ya yi gargadin cewa kada wani dan jam’iyyar APC ya shiga duk wani harin ramuwar gayya domin hakan na iya haifar da rashin tsaro.

Da yake mayar da martani, Mista Kunle Afolayo, mai taimaka wa dan takarar gwamna na jam’iyyar SDP, Yakubu Ajaka, a fannin yada labarai, ya musanta zargin magoya bayan jam’iyyar ne suka kai harin.

“Shin zai yiwu jam’iyyar siyasa ta adawa ta kai wa gwamna hari haka?

“Muna kan hanyarmu ta zuwa fadar Maigari da ke Lokoja daga Koton Karfe a yammacin yau, sai ayarin motocin gwamnan da suka nufi Lokoja daga Abuja suka same mu a hanya, suka kai mana hari.

“Allah ya san gaskiya. Abin takaici ne yadda gwamnatin APC a Kogi ke amfani da karfin gwamnati a kanmu tare da yi mana kazafi kan laifin da suka aikata mana,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AyariHariJami'an TsaroKogiMotociYahaya BelloYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Eritrea Da Takwaransa Na Congo Kinshasa Sun Yabawa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Next Post

Rashin Lafiyar Maigidana Ne Babban Tashin Hankalin Da Na Fuskanta A Vila – Aisha Buhari

Related

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya
Da ɗumi-ɗuminsa

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

2 weeks ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

3 weeks ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

4 weeks ago
Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe
Da ɗumi-ɗuminsa

Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe

1 month ago
Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita
Da ɗumi-ɗuminsa

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita

2 months ago
Fitaccen Malamin Musulunci Mai Da’awar Sunnah A Nijeriya, Dr. Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu
Da ɗumi-ɗuminsa

Fitaccen Malamin Musulunci Mai Da’awar Sunnah A Nijeriya, Dr. Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu

2 months ago
Next Post
Rashin Lafiyar Maigidana Ne Babban Tashin Hankalin Da Na Fuskanta A Vila – Aisha Buhari

Rashin Lafiyar Maigidana Ne Babban Tashin Hankalin Da Na Fuskanta A Vila – Aisha Buhari

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.