• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yansanda 3 Da Wasu A Sakkwato 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yansanda 3 Da Wasu A Sakkwato 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne, a jiya da yamma, sun kai farmaki kauyen ‘Yarbulutu da ke karamar hukumar Sabon Birni a Jihar Sakkwato, inda suka kashe ‘yansanda uku tare da wasu ‘yan kasuwa uku.

Harin ya faru ne da misalin karfe 2:30 na rana a lokacin da shugaban kasa Muhammadu Buhari da ministan tsaro Salihi Magashi ke Sakkwato suna halartar taron shekara-shekara na COAS na 2022.

  • Yankin Arewa Maso Gabashin Nijeriya Na Bukatar Agajin Gaggawa – MDD
  • Fitacciyar Mawakiya Ta Jamhuriyar Nijar Hamsou Garba Ta Rasu

A cewar wani shaidan gani da ido, ‘yan bindigar da suka zo kan babura sun bude wuta kan ‘yan kasuwar da ba su ji ba ba su gani ba a kasuwar mako-mako, lamarin da ya sanya mutane tserewa, inda suka yi kaca-kaca da kasuwar

Jami’an ‘yansandan da ke wani shingen binciken ababen hawa sun garzaya wurin da ‘yan bindigar nan take suka kashe ‘yansanda uku tare da kone wasu motoci guda biyu.

Da yake tabbatar da harin, kakakin rundunar ‘yansandan Jihar Sakkwato, DSP Sanusi Abubakar, ya ce rundunar ta samu rahoton kuma suna farautar maharan domin fuskantar shari’a.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Wani mazaunin kauyen da lamarin ya faru a kan idonsa ya bayyana damuwarsa kan yadda ‘yan bindiga ke ta’addanci a yankin a kullum ba tare da wata turjiya ba.

Ya ce an dade ana tsare da kananan hukumomin Sabon Birni da Isa da ke gabashin Sakkwato domin karbar kudin fansa daga ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane da ke aiki a Zamfara da kuma wani bangare na Jihar Sakkwato.

“Na tabbata wadannan ‘yan bindigar sun fito ne daga Jihar Zamfara kuma yanzu sun koma yankinmu kamar yadda yankin ke da iyaka da jihar a gabas,” in ji ganau.

Idan ba a manta ba a makon jiya ne wasu ‘yan bindiga suka kai hari tare da kashe mutane shida a wani kauye na karamar hukumar Goronyo a jihar.

Irin wannan al’amari ya faru a farkon shekarar da ta gabata inda wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kashe sama da mutane 40.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaSabon BirniSakkwatoYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yankin Arewa Maso Gabashin Nijeriya Na Bukatar Agajin Gaggawa – MDD

Next Post

Ban Taba Nadamar Kai Kara Kotu Kan Takarata Ba – Machina

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

39 minutes ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

17 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 day ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Next Post
Ban Taba Nadamar Kai Kara Kotu Kan Takarata Ba – Machina

Ban Taba Nadamar Kai Kara Kotu Kan Takarata Ba - Machina

LABARAI MASU NASABA

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.