ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Shugaban Kasa: Tinubu, Atiku, Obi Na Dakon Yanke Hukunci

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Kasa

Bayan shafe watanni hudu ana tafka shari’a, kwamitin alkalai na mutum biyar na kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa da ke Abuja, ya saurari karar da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar da takwaransa na jam’iyyar LP, Mista Peter Obi, suka shigar a ranar Talatar da ta gabata inda zai cimma matsaya wajen zartar da hukunci.

Alkalin kotun, Mai Shari’a Haruna Tsammani ya shaida wa masu karar cewa za a sanar da su ranar da za a yanke hukunci. Kotun dai na da wa’adin zartar da hukunci har zuwa ranar 16 ga watan Satumba, bisa ga tanadin kundin tsarin mulkin kasar nan, wanda ya tanadi cewa, dole ne a saurari koke-koken zabe da kuma yanke hukunci cikin kwanaki 180 daga ranar da aka shigar da kara.

  • Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka Na Kara Haifar Da Da Mai Ido
  • An Kammala Harhada Tushen Sashe Na SMR A Sin

A daidai lokacin da Obi ya shigar da karar a ranar 20 ga Maris, Atiku ya shigar da kararsa ne a ranar 21 ga Maris, kusan makonni uku bayan an ayyana Bola Ahmed Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa na ranar 25 ga Fabrairu.

ADVERTISEMENT

Idan ba a manta bai a ranar 1 ga watan Maris ne hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu da kuri’u 8,794,726, yayin da Atiku da Obi suka samu kuri’u 6,984,520 da 6,101,533.

Sai dai kuma Atiku da Obi sun yi watsi da sakamakon zabe. Daga baya sun garzaya kotun sauraron kararrakin zabe domin kalubalantar nasarar Tinubu.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Masu shigar da kara guda biyu sun bukaci kotun ta soke nasarar da Shugaba Tinubu ya samu a kan dalilin da ya sa INEC ta gaza yin dukkan abubuwan da kundin tsarin mulki da dokar zabe ta tanada wajen gudanar da zaben. Sun dai bukaci ko dai kotu ta bai wa daya daga cikinsu ko kuma ta bayar da umurni a sake gudanar da zaben.

Lauyan Atiku, Chris Uche (SAN) ya sanar da kotun cewa babu dalilin da zai sa INEC ta ki yin amfani da na’ura wajen bayyana sakamakon zabe, wanda yana cikin wani bangare na sabon tsarin gudanar da zabe a kasar nan don inganta harkokin zaben Nijeriya. Ya ce rashin bin ka’ida ya turnuke harkokin zaben.

“An saka lamarin cikin sabon dokar zabe, INEC ta tabbatar mana da cewa za a yi amfani da na’urorin a zaben, wanda ka kashe naira biliyan 355 wajen sayo su, don haka ya rage wa INEC ta yi wa ‘yan Nijeriya bayani, ba wai wata matsala ce aka samu ba kawai da gangan aka yi domin yin magudin zabe,” in ji shi.

Shi ma lauyan jam’iyyar LP, Liby Uzoukwu (SAN) ya gabatar da cewa zaben da aka gudanar a rumfunan zabe 18,088, sakamakon zaben ya gurbata, zabe ne mai cike da kura-kurai. Daga cikin takardun sakamakon da INEC ta bai wa masu shigar da kara, 8,123 sun bace, wasu kuma hotuna sun tabbatar da su, ta yaya za su ce sun gudanar da sahihin zabe?

“Duk wani kwafin gaskiya na kowace takarda dole ne ya zama ainihin kwafi, wanda ke bayyana dalilin da ya sa INEC ba za ta iya fitar da asalin takardar sakamakon zabe ba saboda ba zai zama takarda mara amfani,” in ji shi.

Atiku da Obi sun yi zargin cewa rashin tura sakamakon zaben shugaban kasa ga na’ura kai tsaye daga rumfunan zabe ya haifar da rashin bin dokar zabe da ka’idojin INEC tare da samar da hanyar yin magudi.

Sai dai a nasa jawabin, lauyan hukumar INEC, Abubakar Mahmoud (SAN) ya bayya cewa, wadanda suka shigar da kara sun yi tunani a ransu cewa akwai tanadin da aka yi na watsa sakamakon zabe ta na’ura, wanda ba samu damar hakan ba. Ya kara da cewa hujjojinsu sun gaza tabbatar da yadda rashin bin ka’ida ya shafi sakamakon zaben.

Lauyan INEC ya musanta cewa kura-kuran da aka samu a lokacin zabe ba sabon abu ba ne ga na’urorin kuma ba an samu matsalar ba ne sakamakon kutse daga wasu mutane ba ne. Ya ce sakamakon da jam’iyyar LP ta fitar ba na gaskiya ba ne, domin bi yi daidai da ha hukumar zabe ba.

Ya ce amincewa da hujjar da ake bukata na samun kashi 25 cikin 100 a Babban Birnin Tarayya Abuja shirme ne kawai.

Shi kuwa lauyan jam’iyyar APC, Lateef Fagbemi (SAN) ya ce LP ta gaza tabbatar da hujjar rashin tura sakamakon zabe ta na’ura tun daga rumfar zabe. Ya ce ko an sake zaben zai kasance ne tsakanin APC da PDP.

Kasa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Fasahar Zane-zane Na Iya Bunƙasa Samar Da Kuɗaɗen Waje Ga Nijeriya – CIS James 

Fasahar Zane-zane Na Iya Bunƙasa Samar Da Kuɗaɗen Waje Ga Nijeriya - CIS James 

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.