• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zamfara Za Ta Bunƙasa Ta Dawo Matsayinta Na Dandalin Kasuwanci A Arewa – Gwamna Dauda

An ƙaddamar da gagarumin aikin gina babban filin jiragen sama a jihar

by Hussein Yero
1 year ago
zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal ya ƙara jaddada aniyarsa ta sake gina Zamfara don dawo da matsayinta na dandalin kasuwanci a Arewacin Nijeriya.

Gwamnan ya bayar da wannan tabbacin ne a lokacin gudanar da bikin ƙaddamar da fara ginin tashar tashi da saukan jiragen sama, wanda Ministan harkokin Sufurin jiragen sama, Festus Keyamo ya ƙaddamar jiya a Gusau.

  • Garambawul Da Muke Wa Tsarin Aikin Sojojin Nijeriya –Janar Musa

 

A cikin wata sanarwa da Kakakin Gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu jiya, ta bayyana cewa filin jiragen saman da ke Gusau da za a gina, zai zama wani ingantaccen wuri ne da za a rinƙa hidimar harkar jiragen ƙasar nan da na ƙasashen waje.

zamfara

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida

Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho

Kakakin Gwamnan ya ƙara haske da cewa, wannan aiki zai haɗa da gina layin tashin jirage mai kilomita 3.4 don jirage masu zirga-zirga, sanya fitilu a layin, da sauran na’urorin da ke taimaka wa tashi da sauran jirage.

Wani ɓangare na jawabin Gwamna Lawal, ya ƙara jaddada cewa gwamnatin sa ta duƙufa wajen tabbatar da jihar Zamfara ta shiga fagen gogayya a harkokin kasuwanci, wanda zai jawo hankalin masu zuba jari daga ciki da wajen ƙasar nan.

Ya ce, “Mai girma Minista, manyan baƙi, maza da mata, ‘yan jarida, wannan tashar jirgin saman za ta ƙunshi wurin tashin jirage irin na zamani da yanayi mai kyau ga fasinjoji, wanda zai haɗa da wurin tantancewa, wurin duba jakunkuna irin na zamani, wuraren jira, da kuma wuraren jami’an Kwastam da na shige da fice. Bugu da ƙari, tashar nan za ta samu ingantaccen sashen kula da hada-hadar jirage, wanda zai ƙunshi na’urorin sadarwa irin na zamani.

zamfara

“Haka kuma, wurin zai ƙunshi gina sashen kula da gyare-gyare, sashen kashe gobara da ceto, wurin ajiyar man jirgi, hanyoyin zuwa tashar jirgin, wuraren ajiye ababen hawa ga fasinjoji da ma’aikata, samar da isasshe kuma ingantaccen ruwa, isasshiyar wutar lantarki da na’urorin sadarwa.

“Wannan tashar jirgin sama ta Gusau, tsararre ne da zai ƙunshi duk wani fanni na tashi da saukar jirage daga sassan ƙasar nan da na ƙasashen waje, zai zama wata mahaɗa ta yankin. Kowane irin jirgi zai iya sauka a wurin, zai samar da sassauƙar hanyar shiga da fita jihar Zamfara, tare da inganta mu’amala, kasuwanci da yawon buɗe ido.

“Kamfanin gine-gine na ‘Triacta Nigeria Limited’ ne zai gudanar da aikin, bisa shawarar kamfanin ‘JBI Tech Consult’, bisa yarjejeniyar kammala aikin a tsakanin watanni 30.

zamfara

“Akwai amfani mai yawa da ke ƙunshe a harkar gina wannan tashar jirgi ta Gusau, musamman a fannin tattalin arziki, domin zai samar da hanyoyin samun kuɗaɗen shiga da kuma inganta zamantakewa da alaƙa da jihar Zamfara. Zai samar da hanyar shiga jihar mu kai tsaye ta jiragen sama, wanda zai kawar da wahalhalun da ‘yan kasuwa ke sha wajen jigilar hajojin su.”

Tun farko a nasa jawabin, Ministan sufurin jiragen sama na ƙasar nan, Festus Keyamo ya bayyana cewa Zamfara ta kasance koma-baya a harkokin ci gaba, a daidai lokacin da sauran jihohin yankin Arewa maso Yamma su ke da ingantattun filayen jiragen sama, amma ita ba ta da shi, duk da kasancewar ta cibiyar noma a yankin.

Ministan ya ce, “Amma dai ba a makara ba. Wani ɗan jarida daga ƙasar waje ya kira ni yana tambaya ta ko Zamfara na buƙatar tashar jirgin sama. Ina da yaƙinin cewa samar da tashar jiragen sama a Zamfara, ba wai ga haɓaɓaka karkar kasuwanci kawai ya tsaya ba, zai inganta harkar walwala da jin daɗin jama’a. Bisa abubuwan da na lura da su, lallai jihar a shirye ta ke wajen wannan ci gaba.

“Ina so in dawo nan a shekara mai zuwa don ƙaddamar da jigilar maniyyata aikin Hajji. Maniyyatan jihar Zamfara sun kwashe shekaru dama suna shan wahala wajen hawa jirgi zuwa ƙasa mai tsarki. Wannan ba zai sake faruwa ba. Don haka ina tabbatar wa da ɗan uwana, Gwamna Dauda Lawal cewa, ina bayan ka, ina tare da kai, ina tare da al’ummar jihar Zamfara don ganin wannan mafarki ya zama gaskiya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

sallah
Tattalin Arziki

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida

October 11, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho

October 10, 2025
An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 
Tattalin Arziki

An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

October 10, 2025
Next Post
Falalar Ziyarar Kabarin Annabi S.A.W (1)

Falalar Ziyarar Kabarin Annabi S.A.W (1)

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

October 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

October 14, 2025
Asuu

An Janye Wajibcin Samun Kiredit A Darasin Lissafi Ga Ɗaliban Fannin Zamantakewa Don Shiga Manyan Makarantu 

October 14, 2025
Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.