• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zamfara Za Ta Bunƙasa Ta Dawo Matsayinta Na Dandalin Kasuwanci A Arewa – Gwamna Dauda

An ƙaddamar da gagarumin aikin gina babban filin jiragen sama a jihar

by Hussein Yero
1 year ago
in Tattalin Arziki
0
Zamfara Za Ta Bunƙasa Ta Dawo Matsayinta Na Dandalin Kasuwanci A Arewa – Gwamna Dauda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal ya ƙara jaddada aniyarsa ta sake gina Zamfara don dawo da matsayinta na dandalin kasuwanci a Arewacin Nijeriya.

Gwamnan ya bayar da wannan tabbacin ne a lokacin gudanar da bikin ƙaddamar da fara ginin tashar tashi da saukan jiragen sama, wanda Ministan harkokin Sufurin jiragen sama, Festus Keyamo ya ƙaddamar jiya a Gusau.

  • Garambawul Da Muke Wa Tsarin Aikin Sojojin Nijeriya –Janar Musa

 

A cikin wata sanarwa da Kakakin Gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu jiya, ta bayyana cewa filin jiragen saman da ke Gusau da za a gina, zai zama wani ingantaccen wuri ne da za a rinƙa hidimar harkar jiragen ƙasar nan da na ƙasashen waje.

zamfara

Labarai Masu Nasaba

Kungiyar MEMAN Ta Yi Maraba Da Shirin Dangote Na Rabar Da Man Fetur

NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku

Kakakin Gwamnan ya ƙara haske da cewa, wannan aiki zai haɗa da gina layin tashin jirage mai kilomita 3.4 don jirage masu zirga-zirga, sanya fitilu a layin, da sauran na’urorin da ke taimaka wa tashi da sauran jirage.

Wani ɓangare na jawabin Gwamna Lawal, ya ƙara jaddada cewa gwamnatin sa ta duƙufa wajen tabbatar da jihar Zamfara ta shiga fagen gogayya a harkokin kasuwanci, wanda zai jawo hankalin masu zuba jari daga ciki da wajen ƙasar nan.

Ya ce, “Mai girma Minista, manyan baƙi, maza da mata, ‘yan jarida, wannan tashar jirgin saman za ta ƙunshi wurin tashin jirage irin na zamani da yanayi mai kyau ga fasinjoji, wanda zai haɗa da wurin tantancewa, wurin duba jakunkuna irin na zamani, wuraren jira, da kuma wuraren jami’an Kwastam da na shige da fice. Bugu da ƙari, tashar nan za ta samu ingantaccen sashen kula da hada-hadar jirage, wanda zai ƙunshi na’urorin sadarwa irin na zamani.

zamfara

“Haka kuma, wurin zai ƙunshi gina sashen kula da gyare-gyare, sashen kashe gobara da ceto, wurin ajiyar man jirgi, hanyoyin zuwa tashar jirgin, wuraren ajiye ababen hawa ga fasinjoji da ma’aikata, samar da isasshe kuma ingantaccen ruwa, isasshiyar wutar lantarki da na’urorin sadarwa.

“Wannan tashar jirgin sama ta Gusau, tsararre ne da zai ƙunshi duk wani fanni na tashi da saukar jirage daga sassan ƙasar nan da na ƙasashen waje, zai zama wata mahaɗa ta yankin. Kowane irin jirgi zai iya sauka a wurin, zai samar da sassauƙar hanyar shiga da fita jihar Zamfara, tare da inganta mu’amala, kasuwanci da yawon buɗe ido.

“Kamfanin gine-gine na ‘Triacta Nigeria Limited’ ne zai gudanar da aikin, bisa shawarar kamfanin ‘JBI Tech Consult’, bisa yarjejeniyar kammala aikin a tsakanin watanni 30.

zamfara

“Akwai amfani mai yawa da ke ƙunshe a harkar gina wannan tashar jirgi ta Gusau, musamman a fannin tattalin arziki, domin zai samar da hanyoyin samun kuɗaɗen shiga da kuma inganta zamantakewa da alaƙa da jihar Zamfara. Zai samar da hanyar shiga jihar mu kai tsaye ta jiragen sama, wanda zai kawar da wahalhalun da ‘yan kasuwa ke sha wajen jigilar hajojin su.”

Tun farko a nasa jawabin, Ministan sufurin jiragen sama na ƙasar nan, Festus Keyamo ya bayyana cewa Zamfara ta kasance koma-baya a harkokin ci gaba, a daidai lokacin da sauran jihohin yankin Arewa maso Yamma su ke da ingantattun filayen jiragen sama, amma ita ba ta da shi, duk da kasancewar ta cibiyar noma a yankin.

Ministan ya ce, “Amma dai ba a makara ba. Wani ɗan jarida daga ƙasar waje ya kira ni yana tambaya ta ko Zamfara na buƙatar tashar jirgin sama. Ina da yaƙinin cewa samar da tashar jiragen sama a Zamfara, ba wai ga haɓaɓaka karkar kasuwanci kawai ya tsaya ba, zai inganta harkar walwala da jin daɗin jama’a. Bisa abubuwan da na lura da su, lallai jihar a shirye ta ke wajen wannan ci gaba.

“Ina so in dawo nan a shekara mai zuwa don ƙaddamar da jigilar maniyyata aikin Hajji. Maniyyatan jihar Zamfara sun kwashe shekaru dama suna shan wahala wajen hawa jirgi zuwa ƙasa mai tsarki. Wannan ba zai sake faruwa ba. Don haka ina tabbatar wa da ɗan uwana, Gwamna Dauda Lawal cewa, ina bayan ka, ina tare da kai, ina tare da al’ummar jihar Zamfara don ganin wannan mafarki ya zama gaskiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Filin Jirgin SamaKaddamar Da AikiKasuwanciZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A

Next Post

Falalar Ziyarar Kabarin Annabi S.A.W (1)

Related

Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Kungiyar MEMAN Ta Yi Maraba Da Shirin Dangote Na Rabar Da Man Fetur

7 days ago
NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku
Tattalin Arziki

NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku

1 week ago
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

2 weeks ago
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

1 month ago
Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

1 month ago
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

2 months ago
Next Post
Falalar Ziyarar Kabarin Annabi S.A.W (1)

Falalar Ziyarar Kabarin Annabi S.A.W (1)

LABARAI MASU NASABA

Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.