ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zamfara Za Ta Bunƙasa Ta Dawo Matsayinta Na Dandalin Kasuwanci A Arewa – Gwamna Dauda

An ƙaddamar da gagarumin aikin gina babban filin jiragen sama a jihar

by Hussein Yero
2 years ago
zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal ya ƙara jaddada aniyarsa ta sake gina Zamfara don dawo da matsayinta na dandalin kasuwanci a Arewacin Nijeriya.

Gwamnan ya bayar da wannan tabbacin ne a lokacin gudanar da bikin ƙaddamar da fara ginin tashar tashi da saukan jiragen sama, wanda Ministan harkokin Sufurin jiragen sama, Festus Keyamo ya ƙaddamar jiya a Gusau.

  • Garambawul Da Muke Wa Tsarin Aikin Sojojin Nijeriya –Janar Musa

 

ADVERTISEMENT

A cikin wata sanarwa da Kakakin Gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu jiya, ta bayyana cewa filin jiragen saman da ke Gusau da za a gina, zai zama wani ingantaccen wuri ne da za a rinƙa hidimar harkar jiragen ƙasar nan da na ƙasashen waje.

zamfara

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

Kakakin Gwamnan ya ƙara haske da cewa, wannan aiki zai haɗa da gina layin tashin jirage mai kilomita 3.4 don jirage masu zirga-zirga, sanya fitilu a layin, da sauran na’urorin da ke taimaka wa tashi da sauran jirage.

Wani ɓangare na jawabin Gwamna Lawal, ya ƙara jaddada cewa gwamnatin sa ta duƙufa wajen tabbatar da jihar Zamfara ta shiga fagen gogayya a harkokin kasuwanci, wanda zai jawo hankalin masu zuba jari daga ciki da wajen ƙasar nan.

Ya ce, “Mai girma Minista, manyan baƙi, maza da mata, ‘yan jarida, wannan tashar jirgin saman za ta ƙunshi wurin tashin jirage irin na zamani da yanayi mai kyau ga fasinjoji, wanda zai haɗa da wurin tantancewa, wurin duba jakunkuna irin na zamani, wuraren jira, da kuma wuraren jami’an Kwastam da na shige da fice. Bugu da ƙari, tashar nan za ta samu ingantaccen sashen kula da hada-hadar jirage, wanda zai ƙunshi na’urorin sadarwa irin na zamani.

zamfara

“Haka kuma, wurin zai ƙunshi gina sashen kula da gyare-gyare, sashen kashe gobara da ceto, wurin ajiyar man jirgi, hanyoyin zuwa tashar jirgin, wuraren ajiye ababen hawa ga fasinjoji da ma’aikata, samar da isasshe kuma ingantaccen ruwa, isasshiyar wutar lantarki da na’urorin sadarwa.

“Wannan tashar jirgin sama ta Gusau, tsararre ne da zai ƙunshi duk wani fanni na tashi da saukar jirage daga sassan ƙasar nan da na ƙasashen waje, zai zama wata mahaɗa ta yankin. Kowane irin jirgi zai iya sauka a wurin, zai samar da sassauƙar hanyar shiga da fita jihar Zamfara, tare da inganta mu’amala, kasuwanci da yawon buɗe ido.

“Kamfanin gine-gine na ‘Triacta Nigeria Limited’ ne zai gudanar da aikin, bisa shawarar kamfanin ‘JBI Tech Consult’, bisa yarjejeniyar kammala aikin a tsakanin watanni 30.

zamfara

“Akwai amfani mai yawa da ke ƙunshe a harkar gina wannan tashar jirgi ta Gusau, musamman a fannin tattalin arziki, domin zai samar da hanyoyin samun kuɗaɗen shiga da kuma inganta zamantakewa da alaƙa da jihar Zamfara. Zai samar da hanyar shiga jihar mu kai tsaye ta jiragen sama, wanda zai kawar da wahalhalun da ‘yan kasuwa ke sha wajen jigilar hajojin su.”

Tun farko a nasa jawabin, Ministan sufurin jiragen sama na ƙasar nan, Festus Keyamo ya bayyana cewa Zamfara ta kasance koma-baya a harkokin ci gaba, a daidai lokacin da sauran jihohin yankin Arewa maso Yamma su ke da ingantattun filayen jiragen sama, amma ita ba ta da shi, duk da kasancewar ta cibiyar noma a yankin.

Ministan ya ce, “Amma dai ba a makara ba. Wani ɗan jarida daga ƙasar waje ya kira ni yana tambaya ta ko Zamfara na buƙatar tashar jirgin sama. Ina da yaƙinin cewa samar da tashar jiragen sama a Zamfara, ba wai ga haɓaɓaka karkar kasuwanci kawai ya tsaya ba, zai inganta harkar walwala da jin daɗin jama’a. Bisa abubuwan da na lura da su, lallai jihar a shirye ta ke wajen wannan ci gaba.

“Ina so in dawo nan a shekara mai zuwa don ƙaddamar da jigilar maniyyata aikin Hajji. Maniyyatan jihar Zamfara sun kwashe shekaru dama suna shan wahala wajen hawa jirgi zuwa ƙasa mai tsarki. Wannan ba zai sake faruwa ba. Don haka ina tabbatar wa da ɗan uwana, Gwamna Dauda Lawal cewa, ina bayan ka, ina tare da kai, ina tare da al’ummar jihar Zamfara don ganin wannan mafarki ya zama gaskiya.

zamfara
Hussein Yero
+ postsBio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    ’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Ɗan Takarar Sanata A Zamfara Ya Koka Kan Yi Wa Rayuwarsa Barazana
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Abdulaziz Yari Ya Bukaci Limamai Su Ƙara Addu’a Kan Yaƙi Da Ƴan Bindiga A Zamfara

MASU ALAKA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Next Post
Falalar Ziyarar Kabarin Annabi S.A.W (1)

Falalar Ziyarar Kabarin Annabi S.A.W (1)

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.