• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Badakala: Emifiele Ya Sake Shiga Tsaka Mai Wuya Kan Dala Miliyan 6

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Badakala

Tsohon gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele ya sake shiga tsaka mai wuya kan zargin badakalan dala miliyan 6.

Rahotanni sun bayyana cewa binciken da aka gudanar sun tabbatar da cewa ana zargin tsohon gwamnan babban bankin da tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha da wawuredala miliyan 6.3 daga babban bankin Nijeriya lokacin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, wanda aka yi amfani da sa hannunsa wajen fitar da wadannan makudan kudade.

  • Tsawon Shekaru Nawa Tattabaru Ke Yi A Duniya
  • GORON JUMA’A

A cewar rahotannin, an gano cewa an sace wadannan kudade ne a ranar 8 ga Fabrairun 2023, makonni kadan kafin zaben shugaban kasa, inda aka nuna cewa an yi amfani da wadannan kudade ne domin biyan masu saka ido kan zabe na kasashen waje.

A rahotannin dai suna zargin Mustapha tare da Emefiele wajen cire wadannan makudan kudade domin biyan masu saka ido kan zabe na kasashen ketare.

Rahoton bincike dai ya yi ikirarin cewa na’urar CCTB ta nadi yadda aka fitar da kudaden daga CBN.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Hakazalika, gwamnatin tarayya ta bukaci hukumar ‘yansandan kasa da kasa ta INTERPOL ta sanya idanu a kan wasu ‘yan Najeriya uku kan zargin yin takardun bogi.

Majiyoyi sun bayyana cewar ana neman wadanda ake zargin wani jami’in babban bankin Nijeriya, Odoh Ocheme da wasu mutane biyu ruwa a jallo ne a kan zargin kwaikwayar sa hannun tsohon Shugaban Nijeriya, Muhammad Buhari domin satar fiye da dala milyan 6 da dubu 200 daga babban bankin.

Ana zargin Ocheme da kitsa almundahanar tare da yin takardun bogi da sunan Shugaba Buhari domin wawure fiye da dalar amurka milyan 6 da dubu 200 daga asusun babban bankin Nijeriya tare da Adamu Abubakar da Imam Abubakar.

Hakan na kunshe a cikin wata sanarwa mai duke da sa hannun mukaddashin kwamishinan ‘yansanda kuma shugaban sashen kula da ayyuka da bincike na musamman a rundunar ‘yansandan Nijeriya, Oloho Okpoziakpo.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Next Post
Yadda Shan Taba Ke Yi Wa Mata Mummunar Illa

Yadda Shan Taba Ke Yi Wa Mata Mummunar Illa

LABARAI MASU NASABA

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025
Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya

November 2, 2025
An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu

An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu

November 2, 2025
Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

November 2, 2025
A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.