• English
  • Business News
Saturday, June 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Badakala: Emifiele Ya Sake Shiga Tsaka Mai Wuya Kan Dala Miliyan 6

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Rahotonni
0
Kotu Ta Bai Wa Emefiele Damar Yin Tafiye-tafiye A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele ya sake shiga tsaka mai wuya kan zargin badakalan dala miliyan 6.

Rahotanni sun bayyana cewa binciken da aka gudanar sun tabbatar da cewa ana zargin tsohon gwamnan babban bankin da tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha da wawuredala miliyan 6.3 daga babban bankin Nijeriya lokacin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, wanda aka yi amfani da sa hannunsa wajen fitar da wadannan makudan kudade.

  • Tsawon Shekaru Nawa Tattabaru Ke Yi A Duniya
  • GORON JUMA’A

A cewar rahotannin, an gano cewa an sace wadannan kudade ne a ranar 8 ga Fabrairun 2023, makonni kadan kafin zaben shugaban kasa, inda aka nuna cewa an yi amfani da wadannan kudade ne domin biyan masu saka ido kan zabe na kasashen waje.

A rahotannin dai suna zargin Mustapha tare da Emefiele wajen cire wadannan makudan kudade domin biyan masu saka ido kan zabe na kasashen ketare.

Rahoton bincike dai ya yi ikirarin cewa na’urar CCTB ta nadi yadda aka fitar da kudaden daga CBN.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Hakazalika, gwamnatin tarayya ta bukaci hukumar ‘yansandan kasa da kasa ta INTERPOL ta sanya idanu a kan wasu ‘yan Najeriya uku kan zargin yin takardun bogi.

Majiyoyi sun bayyana cewar ana neman wadanda ake zargin wani jami’in babban bankin Nijeriya, Odoh Ocheme da wasu mutane biyu ruwa a jallo ne a kan zargin kwaikwayar sa hannun tsohon Shugaban Nijeriya, Muhammad Buhari domin satar fiye da dala milyan 6 da dubu 200 daga babban bankin.

Ana zargin Ocheme da kitsa almundahanar tare da yin takardun bogi da sunan Shugaba Buhari domin wawure fiye da dalar amurka milyan 6 da dubu 200 daga asusun babban bankin Nijeriya tare da Adamu Abubakar da Imam Abubakar.

Hakan na kunshe a cikin wata sanarwa mai duke da sa hannun mukaddashin kwamishinan ‘yansanda kuma shugaban sashen kula da ayyuka da bincike na musamman a rundunar ‘yansandan Nijeriya, Oloho Okpoziakpo.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wata Mata Ta Taba Zagina A Kan Littafina ‘Umarnin Uba’ —Yareema Shaheed

Next Post

Yadda Shan Taba Ke Yi Wa Mata Mummunar Illa

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

15 hours ago
Badakala
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

7 days ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

1 week ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

2 weeks ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

2 weeks ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

3 weeks ago
Next Post
Yadda Shan Taba Ke Yi Wa Mata Mummunar Illa

Yadda Shan Taba Ke Yi Wa Mata Mummunar Illa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

June 14, 2025
Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su

Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su

June 14, 2025
DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

June 14, 2025
Tinubu

Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa

June 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci

June 14, 2025
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

June 14, 2025
Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

June 14, 2025
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

June 14, 2025
APC

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

June 14, 2025
Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

June 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.