• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Badakala: Emifiele Ya Sake Shiga Tsaka Mai Wuya Kan Dala Miliyan 6

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Badakala

Tsohon gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele ya sake shiga tsaka mai wuya kan zargin badakalan dala miliyan 6.

Rahotanni sun bayyana cewa binciken da aka gudanar sun tabbatar da cewa ana zargin tsohon gwamnan babban bankin da tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha da wawuredala miliyan 6.3 daga babban bankin Nijeriya lokacin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, wanda aka yi amfani da sa hannunsa wajen fitar da wadannan makudan kudade.

  • Tsawon Shekaru Nawa Tattabaru Ke Yi A Duniya
  • GORON JUMA’A

A cewar rahotannin, an gano cewa an sace wadannan kudade ne a ranar 8 ga Fabrairun 2023, makonni kadan kafin zaben shugaban kasa, inda aka nuna cewa an yi amfani da wadannan kudade ne domin biyan masu saka ido kan zabe na kasashen waje.

A rahotannin dai suna zargin Mustapha tare da Emefiele wajen cire wadannan makudan kudade domin biyan masu saka ido kan zabe na kasashen ketare.

Rahoton bincike dai ya yi ikirarin cewa na’urar CCTB ta nadi yadda aka fitar da kudaden daga CBN.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Hakazalika, gwamnatin tarayya ta bukaci hukumar ‘yansandan kasa da kasa ta INTERPOL ta sanya idanu a kan wasu ‘yan Najeriya uku kan zargin yin takardun bogi.

Majiyoyi sun bayyana cewar ana neman wadanda ake zargin wani jami’in babban bankin Nijeriya, Odoh Ocheme da wasu mutane biyu ruwa a jallo ne a kan zargin kwaikwayar sa hannun tsohon Shugaban Nijeriya, Muhammad Buhari domin satar fiye da dala milyan 6 da dubu 200 daga babban bankin.

Ana zargin Ocheme da kitsa almundahanar tare da yin takardun bogi da sunan Shugaba Buhari domin wawure fiye da dalar amurka milyan 6 da dubu 200 daga asusun babban bankin Nijeriya tare da Adamu Abubakar da Imam Abubakar.

Hakan na kunshe a cikin wata sanarwa mai duke da sa hannun mukaddashin kwamishinan ‘yansanda kuma shugaban sashen kula da ayyuka da bincike na musamman a rundunar ‘yansandan Nijeriya, Oloho Okpoziakpo.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Next Post
Yadda Shan Taba Ke Yi Wa Mata Mummunar Illa

Yadda Shan Taba Ke Yi Wa Mata Mummunar Illa

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

November 8, 2025
NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

November 8, 2025
Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

November 8, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

November 8, 2025
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.