Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Zargin Kada Kuri’u Na Yara: Kwamitin INEC Ya Gabatar Da Rahotonsa

by
4 years ago
in RAHOTANNI
2 min read
Sabuwar Jam’iyyar BNPP Ta Shiga Da Kafar Dama A Yobe, In Ji Gishuwa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Khalid Idris Doya, Abuja

Kwamitin nan da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta kafa domin bincikar hakikanin zargin da ake yi na cewar yara ‘yan kasa da shekaru 18 sun samu zarafin kada kuri’a a zaben kananan hukumomi da ya guda a jihar Kano kwanaki, wanda hukumar zabe ta jihar Kano (KIDC) ta shirya, kwamitin ya kammala aikinsa hade da mika rahoton binciken da ya yi.

Kwamitin, kamar yadda bayanin ke kunshe a cikin sanarwar da Daraktar yadawa, fadakarwa da kuma ilmantar da jama’a na hukumar ta INEC Mr Oluwole Osaze-Uzzi ya sanya wa hanu gami da rabawa manema labaru a Abuja, ya ce kwamitin ya mika rahoton aikin da aka sanya shi ne wa shugaban INEC ta kasa Farfesa Mahmood Yakubu, a ranar Juma’a.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

Fashewar Gas A Kano: Ministar Jinkai Ta Nemi A Dauki Matakan Riga-kafi

A lokacin da ke mika rahoton, shugaban kwamitin, Ahmed Nahuche, ya shaida wa shugaban INEC Mahmood Yakubu cewar sun yi zazzafar bincike gami da gayyatar dukkanin wadanda lamarin ya shafa zuwa gaban kwamitin domin bayar da bahasin abun da suka gani ya wakana a wajen zaben.

Wannan kwamitin dai INEC ce ta kaddamar da ita a watan Fabrairu da nufin ya binciko hakikanin zargin da ake yi na cewar yaran da basu kai shekarun kada kuri’a ba sun kada dauke da karin zabe a Kano.

Nahuche Ya ce, daga lokaci lokacin da suka amshi aikin sun gayyaci dukkanin wadanda abun ya shafa don tattaunawa gami da jin bahasi “wannan ganawar jin bahasin ta kunshi bangarorin kungiyoyin fararen huda, jam’iyyun siyasa, ‘yan jaridu na takarda da na na’ura, kungiyoyi ciki kuwa har da jami’an tsaro,”

“Kwamitinmu a sakamakon wannan ganawar da kuma gayyatar wadanda suka dace, mun samu hotuna, da kuma hotuna masu motsi, rahotonni, kundin adana, da kuma gabatar da bayanai daga wadanda abun ya shafa a jihar,”

“Nan da nan muka fara aikin ganowa da kuma binciken yadda aka gudanar da zaben kananan hukumomi na Kano wanda KASIEC ta gudanar,”

Ya ce “Kwamitin ya maida hankali wajen binciken hakikanin rahotonin da kafafen sadarwar zamani suka yada na hotona da hotuna masu motsi wadda ke cewa ana zargin yaran da basu kai munzalin kada kuri’a ba sun halarci wajen zaben kananan hukumomi a Kano, wanda wannan zancen ta tayar da kura sosai, don haka bincikenmu ya maida hakali kan wannan lamarin,”

“Hotunan mun yi musu dogon nazari a kansu, kwamitin nan ya tsaya sosai yak all hotunan da idon basira gaya,”

Nahuche ya kuma bukaci hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Kano da sauran jam’iyyun siyasa da su tabbatar da karfafar bin dokokin zabe domin gabbatar da ingancin da kuma bin hanyoyin da suka dace.

Ya bukaci jam’iyyun siyasa a kasar nan da su kasance masu yin ababen da zai kai ga samun ribar demokradiyya ba kokarin tarwatsa jin dadin shi demokradyyar ba.

Da ya ke amsar rahoton, shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa Prof. Mahmood Yakubu ya jinjina wa kwamitin a bisa gudanar da aikin da aka daura masa, yana mai cewa hidimar da ta shafi harkar katin zabe abu ne wanda hukumarsu bata wasa ko kadan da shi don haka ne ya nemi jama’a da su ma su dauki lamarin da muhimmanci.

Idan dai baku mance ba, Bayan gudanar da zaben kananan hukumomin jihar Kano ne dai wasu hotuna suka yi ta yawa na cewar ga yara kankana suna kokarin dangala kuri’a, wanda lamarin ta janyo ala tilas INEC ta kafa kwamitin bincike.

 

Like this:

Like Loading...
Tags: Zargin Kada Kuri’u Na Yara
SendShareTweetShare
Previous Post

Wani Kasaitaccen Sarki A Nijeriya Ya Na Zamanantar Da Birninsa

Next Post

PDP Ta Yi Bazaranar Maka Gwamnatin Kano A Kotu Kan Hana Gangami

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

by Ahmed Muhammad Dan'asabe
19 hours ago
0

...

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

Fashewar Gas A Kano: Ministar Jinkai Ta Nemi A Dauki Matakan Riga-kafi

by
21 hours ago
0

...

Baki Biyu Bai Dace Da Matsayin Amurka Ba

Baki Biyu Bai Dace Da Matsayin Amurka Ba

by CMG Hausa
23 hours ago
0

...

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

by
3 days ago
0

...

Next Post
PDP Ta Sha Alwashin Kwace Legas A 2019

PDP Ta Yi Bazaranar Maka Gwamnatin Kano A Kotu Kan Hana Gangami

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: