• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ziyarar Jiragen Ruwan Soji Na Sin A Nijeriya Ta Zo A Lokaci Mafi Dacewa

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ziyarar Jiragen Ruwan Soji Na Sin A Nijeriya Ta Zo A Lokaci Mafi Dacewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani yunkuri na karfafa hulda da abota tsakanin Sin da Nijeriya, jiragen sojin ruwan kasar Sin 3, sun isa Legas na Nijeriya a jiya Litinin, da zummar karfafa tsaron teku a yankin.

Zan iya cewa, wannan ziyara ce ta karfafa tsaron teku bisa la’akari da zuwanta a kan gaba, wato watanni 6 bayan Nijeriya ta kaddamar da tashar jiragen ruwa mai zurfi dake Lekki na jihar Lagos, wanda ke zama wata katafariyar hanyar bunkasa cinikayya da bunkasa tattalin arzikin kasar, da ma jan hankalin karin masu zuba jari daga ketare. Har ila yau, ba za a taba raba nasarar kafuwar wannan katafariyar tasha da tallafin kasar Sin ba, lamarin dake kara nuna amincin dake tsakanin Sin da Nijeriya da ma yadda kasar Sin din ke da kwarin gwiwa kan ci gaban Nijeriya. Wannan ya sake bayyana matsayin Sin na aminiyar dake ingiza ci gaban ’yan uwanta kasashe masu tasowa.

  • Xi Jinping: Ba Za’a Iya Hana Ayyukan Shimfida Zaman Lafiya Da Samar Da Ci Gaba Da Inganta Hadin-Gwiwa Da Cimma Moriya Tare Ba

A matsayinta na irinta mafi girma a yankin, tabbatar da ganin cikar burin kafa wannan tasha da dimbin alfanun dake tattare da ita, na matukar bukatar tsaro. Dole ne batun tsaro ya zama a kan gaba bisa la’akari da yadda yankin ke fama da matsalar fashin teku. Tabbatuwar tsaro ita ce za ta kai ga samun kyawawan sakamakon da ake buri.

Sin tana da gogewa ta fuskar tsaro a cikin gida da ma iyakokinta, har da ma sauran sassan duniya da take aikin tabbatar da zaman lafiya, yayin da Nijeriya ke fuskantar matsaloli daban-daban a bangaren, kuma fashin teku na daya daga cikinsu. Muna sa ran ziyarar kwanaki 5 ta jirage da sojojin ruwan Sin a Nijeriya, za ta inganta samar da hanyoyin shawo kan matsalar fashin teku da ake fuskanta a Nijeriyar, wanda ke kai wa ga garkuwa da baki ’yan kasashen waje domin neman kudin fansa ko ma asarar rayuka da dukiyoyi.

Duk da cewa masharhanta na ganin wannan lamari ba zai yi wa kasashen yamma dadi ba, ba shakka Nijeriya da ma yankin yammacin Afrika, na bukatar tallafin tsaro da duk wani yunkuri da zai tabbatar da kwanciyar hankali da gudanar da al’amura yadda ya kamata, kuma kasar Sin ta nuna cewa a shirye take ta share musu hawaye.

Labarai Masu Nasaba

Hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Dole kasar Sin ta ci gaba da samun karbuwa a tsakanin kasashe masu tasowa, musamman ma na Afrika, domin ta nuna ta damu da yanayin da suke ciki, kuma tana iyakar kokarinta na ganin ta samar musu mafita cikin ruwan sanyi kuma bisa adalci da girmamawa. Don haka, wannan ziyara ta zo a kan gaba, domin za ta amfanawa Nijeriya da ma sauran kasashen yankin yammacin Afrika.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Samar Da Motoci Masu Amfani Da Wutar Lantarki Miliyan 20

Next Post

Hukumar Kashe Gobara Ta Kano Ta Ceci Rayuka 26, Da Dukiyar Miliyan ₦17 A Cikin Watan Yuni

Related

Hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu
Daga Birnin Sin

Hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

34 minutes ago
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

3 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

3 hours ago
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare
Daga Birnin Sin

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

15 hours ago
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali
Daga Birnin Sin

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

16 hours ago
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani
Daga Birnin Sin

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

17 hours ago
Next Post
Hukumar Kashe Gobara Ta Kano Ta Ceci Rayuka 26, Da Dukiyar Miliyan ₦17 A Cikin Watan Yuni

Hukumar Kashe Gobara Ta Kano Ta Ceci Rayuka 26, Da Dukiyar Miliyan ₦17 A Cikin Watan Yuni

LABARAI MASU NASABA

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.