• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ziyarar Jiragen Ruwan Soji Na Sin A Nijeriya Ta Zo A Lokaci Mafi Dacewa

by CMG Hausa
2 years ago
Sin

A wani yunkuri na karfafa hulda da abota tsakanin Sin da Nijeriya, jiragen sojin ruwan kasar Sin 3, sun isa Legas na Nijeriya a jiya Litinin, da zummar karfafa tsaron teku a yankin.

Zan iya cewa, wannan ziyara ce ta karfafa tsaron teku bisa la’akari da zuwanta a kan gaba, wato watanni 6 bayan Nijeriya ta kaddamar da tashar jiragen ruwa mai zurfi dake Lekki na jihar Lagos, wanda ke zama wata katafariyar hanyar bunkasa cinikayya da bunkasa tattalin arzikin kasar, da ma jan hankalin karin masu zuba jari daga ketare. Har ila yau, ba za a taba raba nasarar kafuwar wannan katafariyar tasha da tallafin kasar Sin ba, lamarin dake kara nuna amincin dake tsakanin Sin da Nijeriya da ma yadda kasar Sin din ke da kwarin gwiwa kan ci gaban Nijeriya. Wannan ya sake bayyana matsayin Sin na aminiyar dake ingiza ci gaban ’yan uwanta kasashe masu tasowa.

  • Xi Jinping: Ba Za’a Iya Hana Ayyukan Shimfida Zaman Lafiya Da Samar Da Ci Gaba Da Inganta Hadin-Gwiwa Da Cimma Moriya Tare Ba

A matsayinta na irinta mafi girma a yankin, tabbatar da ganin cikar burin kafa wannan tasha da dimbin alfanun dake tattare da ita, na matukar bukatar tsaro. Dole ne batun tsaro ya zama a kan gaba bisa la’akari da yadda yankin ke fama da matsalar fashin teku. Tabbatuwar tsaro ita ce za ta kai ga samun kyawawan sakamakon da ake buri.

Sin tana da gogewa ta fuskar tsaro a cikin gida da ma iyakokinta, har da ma sauran sassan duniya da take aikin tabbatar da zaman lafiya, yayin da Nijeriya ke fuskantar matsaloli daban-daban a bangaren, kuma fashin teku na daya daga cikinsu. Muna sa ran ziyarar kwanaki 5 ta jirage da sojojin ruwan Sin a Nijeriya, za ta inganta samar da hanyoyin shawo kan matsalar fashin teku da ake fuskanta a Nijeriyar, wanda ke kai wa ga garkuwa da baki ’yan kasashen waje domin neman kudin fansa ko ma asarar rayuka da dukiyoyi.

Duk da cewa masharhanta na ganin wannan lamari ba zai yi wa kasashen yamma dadi ba, ba shakka Nijeriya da ma yankin yammacin Afrika, na bukatar tallafin tsaro da duk wani yunkuri da zai tabbatar da kwanciyar hankali da gudanar da al’amura yadda ya kamata, kuma kasar Sin ta nuna cewa a shirye take ta share musu hawaye.

LABARAI MASU NASABA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Dole kasar Sin ta ci gaba da samun karbuwa a tsakanin kasashe masu tasowa, musamman ma na Afrika, domin ta nuna ta damu da yanayin da suke ciki, kuma tana iyakar kokarinta na ganin ta samar musu mafita cikin ruwan sanyi kuma bisa adalci da girmamawa. Don haka, wannan ziyara ta zo a kan gaba, domin za ta amfanawa Nijeriya da ma sauran kasashen yankin yammacin Afrika.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal
Daga Birnin Sin

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025
Daga Birnin Sin

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
Next Post
Hukumar Kashe Gobara Ta Kano Ta Ceci Rayuka 26, Da Dukiyar Miliyan ₦17 A Cikin Watan Yuni

Hukumar Kashe Gobara Ta Kano Ta Ceci Rayuka 26, Da Dukiyar Miliyan ₦17 A Cikin Watan Yuni

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

October 10, 2025
Sin

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

October 10, 2025
Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

October 10, 2025
Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

October 10, 2025
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.