ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ziyarar Jiragen Ruwan Soji Na Sin A Nijeriya Ta Zo A Lokaci Mafi Dacewa

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

A wani yunkuri na karfafa hulda da abota tsakanin Sin da Nijeriya, jiragen sojin ruwan kasar Sin 3, sun isa Legas na Nijeriya a jiya Litinin, da zummar karfafa tsaron teku a yankin.

Zan iya cewa, wannan ziyara ce ta karfafa tsaron teku bisa la’akari da zuwanta a kan gaba, wato watanni 6 bayan Nijeriya ta kaddamar da tashar jiragen ruwa mai zurfi dake Lekki na jihar Lagos, wanda ke zama wata katafariyar hanyar bunkasa cinikayya da bunkasa tattalin arzikin kasar, da ma jan hankalin karin masu zuba jari daga ketare. Har ila yau, ba za a taba raba nasarar kafuwar wannan katafariyar tasha da tallafin kasar Sin ba, lamarin dake kara nuna amincin dake tsakanin Sin da Nijeriya da ma yadda kasar Sin din ke da kwarin gwiwa kan ci gaban Nijeriya. Wannan ya sake bayyana matsayin Sin na aminiyar dake ingiza ci gaban ’yan uwanta kasashe masu tasowa.

  • Xi Jinping: Ba Za’a Iya Hana Ayyukan Shimfida Zaman Lafiya Da Samar Da Ci Gaba Da Inganta Hadin-Gwiwa Da Cimma Moriya Tare Ba

A matsayinta na irinta mafi girma a yankin, tabbatar da ganin cikar burin kafa wannan tasha da dimbin alfanun dake tattare da ita, na matukar bukatar tsaro. Dole ne batun tsaro ya zama a kan gaba bisa la’akari da yadda yankin ke fama da matsalar fashin teku. Tabbatuwar tsaro ita ce za ta kai ga samun kyawawan sakamakon da ake buri.

ADVERTISEMENT

Sin tana da gogewa ta fuskar tsaro a cikin gida da ma iyakokinta, har da ma sauran sassan duniya da take aikin tabbatar da zaman lafiya, yayin da Nijeriya ke fuskantar matsaloli daban-daban a bangaren, kuma fashin teku na daya daga cikinsu. Muna sa ran ziyarar kwanaki 5 ta jirage da sojojin ruwan Sin a Nijeriya, za ta inganta samar da hanyoyin shawo kan matsalar fashin teku da ake fuskanta a Nijeriyar, wanda ke kai wa ga garkuwa da baki ’yan kasashen waje domin neman kudin fansa ko ma asarar rayuka da dukiyoyi.

Duk da cewa masharhanta na ganin wannan lamari ba zai yi wa kasashen yamma dadi ba, ba shakka Nijeriya da ma yankin yammacin Afrika, na bukatar tallafin tsaro da duk wani yunkuri da zai tabbatar da kwanciyar hankali da gudanar da al’amura yadda ya kamata, kuma kasar Sin ta nuna cewa a shirye take ta share musu hawaye.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Dole kasar Sin ta ci gaba da samun karbuwa a tsakanin kasashe masu tasowa, musamman ma na Afrika, domin ta nuna ta damu da yanayin da suke ciki, kuma tana iyakar kokarinta na ganin ta samar musu mafita cikin ruwan sanyi kuma bisa adalci da girmamawa. Don haka, wannan ziyara ta zo a kan gaba, domin za ta amfanawa Nijeriya da ma sauran kasashen yankin yammacin Afrika.

Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Next Post
Hukumar Kashe Gobara Ta Kano Ta Ceci Rayuka 26, Da Dukiyar Miliyan ₦17 A Cikin Watan Yuni

Hukumar Kashe Gobara Ta Kano Ta Ceci Rayuka 26, Da Dukiyar Miliyan ₦17 A Cikin Watan Yuni

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.