ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Sabon Shugaban PDP Zai Iya Magance Matsalolin Jam’iyyar Kuwa?

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
4 weeks ago
PDP

Garin Ibadan, babban birnin Jihar Oyo, ya karbi bakuncin daruruwan wakilai a babban taron jam’iyyar PDP mai cike da cece-kuce, inda dubban ‘yan jam’iyya da gwamnonin hudu suka taru a filin wasa na Lekan Salami, Adamasingba.

Wannan taron na tsawon kwanaki biyu daga ranar Asabar, 15 ga Nuwamba har zuwa safiyar Lahadi, 16 ga Nuwamba, 2025, an dai gudanar da abubawa masu yawa da suka hada da raye-raye da kade-kade tare da lika hotunan ‘ya’yan jam’iyya wadanda ke neman mukamai daban-daban a cikin filin wasan.

  • Allah Ya Tsarkake Iyalan Annabi (SAW) Daga Kazanta
  • Gwamnan Neja Ya Yi Allah-Wadai Da Sace Ɗaliban St. Mary A Papiri

Domin tabbatar da cewa an gudanar da taron ba tare da matsala ba, jami’an tsaron ‘yansanda da jami’an tsaro na farin kaya (DSS) da rundunar Amotekun ta Jihar Oyo sun tsare manyan wurare a kusa da filin wasa, yayin da jami’an kula da zirga-zirga ke aiki ba dare ba rana don sarrafa yawan motoci a kan Titin Obafemi Awolowo da titunan kusa da shi.

ADVERTISEMENT

Alamar farko na rashin jituwa a taron dai shi ne, yadda fusatattun ‘ya’yan jam’iyyar suka dunga yage hotunan gwamnonin PDP guda biyu, Ademola Adeleke na Jihar Osun da Agbu Kefas na Jihar Taraba wadanda ba su halarci taron ba.

Gwamnonin da suka halarci taron sun hada da Ahmadu Fintiri (Adamawa); Caleb Muftwang (Filato); Bala Mohammed (Bauchi); Dauda Lawal (Zamfara) da kuma mai masaukin baki, Seyi Makinde na Jihar Oyo.

LABARAI MASU NASABA

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama

Taron kuma ya jawo shahararrun ‘yan PDP kamar tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Adolphus Wabara da Cif Olabode George da tsofaffin gwamnoni irinsu Udom Emmanuelda Babangida Aliyu da Ibrahim Shekarau, da sauran manyan ‘yan jam’iyyar.

Shugaban kwamitin shirya taron kuma Gwamnan Jihar Adamawa, Umaru Fintiri, yayin da yake jawabi a taron, ya ce ‘yan Nijeriya za su sake kallon PDP don ceto kasa.

A cewarsa, “Ikon jam’iyya na nufin jam’iyya da aka gina sosai bisa ka’idojin karfin zuciya da kiraye-kiraye na dimokuradiyya domin ceto Nijeriya. Kuma a kowane lokaci bai kamata ta sauka daga layin da ka kafa ta ba.

“Nijeriya da ‘yan Nijeriya har yanzu suna kallonmu a matsayin wadanda suka taka rawa da ya dace da tsarin jam’iyyarmu. Hakika, Nijeriya ta koma baya tun lokacin da APC ta amshi mulki. Dole ne mu yarda cewa duk munanan abubuwan da suka faru a Nijeriya a cikin ‘yan shekarun nan sun shafi jam’iyyarmu. Ruhin jam’iyya har yanzu bai lalace ba saboda akwai maza da mata da suka yi imani da ginshikan jam’iyya.”

A nasa jawabin, Gwamna Makinde ya bayyana cewa babban taron Ibadan na 2025 za a dunga tunawa da shi a matsayin  wani abu mai matukar muhimmanci ga jam’iyya.

Ya ce, “Ina so in yi garsuwar maraba da kowa zuwa wannan taro, musamman mambobin PDP masu juriya. Bari in yi amfani da wannan dama don yin maraba da ku zuwa Ibadan, Jihar Oyo. Mun yi dogon gwagwarmaya don isa wannan matakin, amma ga mu a nan. Kuma da ni’imar Allah, wannan taro zai kasance taron da ya kawo juyin-juya hali ga PDP a kasa baki daya.”

Yayin da yake magana a madadin kungiyar gwamnonin PDP, Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jaddada hadin kan gwamnonin jam’iyyar. Ya ce, “Kamar yadda kuke gani, muna nan a yau a matsayin kungiya ta hadin kai don ci gaban wannan jam’iyya. Muna rokon kowa da kowa da ke nan da ya ba mu cikakken goyon baya domin mu ceci makomar Nijeriya. Ina fatan wannan babban taron ya yi nasara.”

A cikin sakon fatan alheri, shugaban kwamitin amintattu PDP, Sanata Adolphus Wabara, ya bayyana taron a matsayin babban nasara ga jam’iyyar. A cewarsa, jam’iyyar ba za ta shude ba saboda taron ya kasance shaida ga juriyar mambobinta, ruhin dimokuradiyya da hadin gwiwar da mambobi ke da shi wajen bin ka’idodi da ci gaban Nijeriya, yana karfafa mambobin kwamitin gudanarwa su kasance masu rungumar shugabanci na gari don samun hadin kai.

Daya daga cikin muhimmancin sakamakon taron shi ne, korar wasu manyan mambobi saboda zargin ayyukan da suka saba wa jam’iyya. Wadanda aka kora sun hada da Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike da sakataren jam’iyyar, Samuel Anyanwu da tsohon gwamnan Jihar Ekiti, Ayodele Fayose da mashawarcin shari’a na jam’iyya, Adeyemi Ajibade (SAN) da Umar Bature da AbdulRahman Mohammed da Mao Ohuambuwa da George Turner da Austin Nwachukwu da Abraham Ammah da kuma Dan Orbih.

Babban abin da taron ya kunsa shi ne zaben babban lauya daga Jihar Kebb, Kabiru Turaki a matsayin sabon shugaban jam’iyyar PDP. Sakatare taron, Sanata Ben Obi ya bayyana cewa Turaki ya samu kuri’u 1,516, wanda ya ba shi damar zama sabon shugaban PDP.

Haka kuma an zabi Mista Solarin Adekunle, a matsayin mataimakin sakataren tsare-tsaren al’amura na jam’iyyar, yayin da wasu ‘yan takara da dama suka sami dawowa mukamansu ba tare da hamayyar ba bayan janye ‘yan adawarsu.

A cikin jawabinsa na karbar mukami, Turaki ya ce ya fahimci girman nauyin da aka dora a wuyansa da na jagorantar kwamitin gudanarwa na jam’iyyar, yana mai kara cewa wajibi ne su cika aikin da aka dora musu ga ‘yan Nijeriya cikin aminci.

Ya bayyana cewa sabuwar shugabanci za ta fitar da ka’idojinta da tsarin aiki nan ba da jimawa ba, tare da jaddada cewa kwamitin zai fara aiki nan take. Yayin da yake jaddada cewa PDP ce kadai jam’iyyar siyasa a kasar da ta kiyaye asalinta tun farkon kafuwarta.

Ya ce, “Nauyin da kuka dora mana yana nufin cewa kuna kallo mu don mu kai ga ciki ga mutanen Nijeriya, kuma za mu yi haka. Ba mu yin tunanin karya cewa aikin da aka ba mu abu ne mai sauki. Jam’iyyarmu na cikin wani yanayi mai wahala yanzu, amma muna da karfin yin aikin da kuma karfin fuskantar kalubale.

“Ba da dadewa ba, za mu bayyana mene ne ka’idodinmu masu jagoranci da kuma yadda za mu cimma su. Lokacin da muke yin hakan, za mu fara aiki cikin sauri tun daga ranar farko. Yau, yayin da nake magana da ku, jam’iyyar siyasa daya tilo da ta ci gaba da rike sunanta ita ce jam’iyyar PDP. Wannan ya yiwu ne saboda wannan jam’iyya ce ta mutanen Nijeriya.”

Abin da ba a yi shakka a kai ba shi ne, babban taron ya gudana ne bisa saba wa hukuncin kotu da suka yi kokarin dakatar da shi, yayin da wakilai da masu jawabi daban-daban suka koma kan batun shari’o’in. Duk da haka, ga masu lura da siyasa, lokaci ne kawai zai nuna ko sakamakon zai taimaka wajen kawo karshen rikice-rikicen da ke damun jam’iyyar ko kuwa zai kara haddasa su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC

December 19, 2025
‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama

December 19, 2025
Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027
Tambarin Dimokuradiyya

NNPP Ta Buƙaci INEC Ta Yi Watsi Da Tarukan Jam’iyyar Da Kwankwaso Zai Jagoranta

November 28, 2025
Next Post
NDLEA Ta Cafke Mutane 230 Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

NDLEA Ta Cafke Mutane 230 Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

LABARAI MASU NASABA

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.