ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Sabon Shugaban PDP Zai Iya Magance Matsalolin Jam’iyyar Kuwa?

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
10 months ago
PDP

Garin Ibadan, babban birnin Jihar Oyo, ya karbi bakuncin daruruwan wakilai a babban taron jam’iyyar PDP mai cike da cece-kuce, inda dubban ‘yan jam’iyya da gwamnonin hudu suka taru a filin wasa na Lekan Salami, Adamasingba.

Wannan taron na tsawon kwanaki biyu daga ranar Asabar, 15 ga Nuwamba har zuwa safiyar Lahadi, 16 ga Nuwamba, 2025, an dai gudanar da abubawa masu yawa da suka hada da raye-raye da kade-kade tare da lika hotunan ‘ya’yan jam’iyya wadanda ke neman mukamai daban-daban a cikin filin wasan.

  • Allah Ya Tsarkake Iyalan Annabi (SAW) Daga Kazanta
  • Gwamnan Neja Ya Yi Allah-Wadai Da Sace Ɗaliban St. Mary A Papiri

Domin tabbatar da cewa an gudanar da taron ba tare da matsala ba, jami’an tsaron ‘yansanda da jami’an tsaro na farin kaya (DSS) da rundunar Amotekun ta Jihar Oyo sun tsare manyan wurare a kusa da filin wasa, yayin da jami’an kula da zirga-zirga ke aiki ba dare ba rana don sarrafa yawan motoci a kan Titin Obafemi Awolowo da titunan kusa da shi.

ADVERTISEMENT

Alamar farko na rashin jituwa a taron dai shi ne, yadda fusatattun ‘ya’yan jam’iyyar suka dunga yage hotunan gwamnonin PDP guda biyu, Ademola Adeleke na Jihar Osun da Agbu Kefas na Jihar Taraba wadanda ba su halarci taron ba.

Gwamnonin da suka halarci taron sun hada da Ahmadu Fintiri (Adamawa); Caleb Muftwang (Filato); Bala Mohammed (Bauchi); Dauda Lawal (Zamfara) da kuma mai masaukin baki, Seyi Makinde na Jihar Oyo.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

Taron kuma ya jawo shahararrun ‘yan PDP kamar tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Adolphus Wabara da Cif Olabode George da tsofaffin gwamnoni irinsu Udom Emmanuelda Babangida Aliyu da Ibrahim Shekarau, da sauran manyan ‘yan jam’iyyar.

Shugaban kwamitin shirya taron kuma Gwamnan Jihar Adamawa, Umaru Fintiri, yayin da yake jawabi a taron, ya ce ‘yan Nijeriya za su sake kallon PDP don ceto kasa.

A cewarsa, “Ikon jam’iyya na nufin jam’iyya da aka gina sosai bisa ka’idojin karfin zuciya da kiraye-kiraye na dimokuradiyya domin ceto Nijeriya. Kuma a kowane lokaci bai kamata ta sauka daga layin da ka kafa ta ba.

“Nijeriya da ‘yan Nijeriya har yanzu suna kallonmu a matsayin wadanda suka taka rawa da ya dace da tsarin jam’iyyarmu. Hakika, Nijeriya ta koma baya tun lokacin da APC ta amshi mulki. Dole ne mu yarda cewa duk munanan abubuwan da suka faru a Nijeriya a cikin ‘yan shekarun nan sun shafi jam’iyyarmu. Ruhin jam’iyya har yanzu bai lalace ba saboda akwai maza da mata da suka yi imani da ginshikan jam’iyya.”

A nasa jawabin, Gwamna Makinde ya bayyana cewa babban taron Ibadan na 2025 za a dunga tunawa da shi a matsayin  wani abu mai matukar muhimmanci ga jam’iyya.

Ya ce, “Ina so in yi garsuwar maraba da kowa zuwa wannan taro, musamman mambobin PDP masu juriya. Bari in yi amfani da wannan dama don yin maraba da ku zuwa Ibadan, Jihar Oyo. Mun yi dogon gwagwarmaya don isa wannan matakin, amma ga mu a nan. Kuma da ni’imar Allah, wannan taro zai kasance taron da ya kawo juyin-juya hali ga PDP a kasa baki daya.”

Yayin da yake magana a madadin kungiyar gwamnonin PDP, Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jaddada hadin kan gwamnonin jam’iyyar. Ya ce, “Kamar yadda kuke gani, muna nan a yau a matsayin kungiya ta hadin kai don ci gaban wannan jam’iyya. Muna rokon kowa da kowa da ke nan da ya ba mu cikakken goyon baya domin mu ceci makomar Nijeriya. Ina fatan wannan babban taron ya yi nasara.”

A cikin sakon fatan alheri, shugaban kwamitin amintattu PDP, Sanata Adolphus Wabara, ya bayyana taron a matsayin babban nasara ga jam’iyyar. A cewarsa, jam’iyyar ba za ta shude ba saboda taron ya kasance shaida ga juriyar mambobinta, ruhin dimokuradiyya da hadin gwiwar da mambobi ke da shi wajen bin ka’idodi da ci gaban Nijeriya, yana karfafa mambobin kwamitin gudanarwa su kasance masu rungumar shugabanci na gari don samun hadin kai.

Daya daga cikin muhimmancin sakamakon taron shi ne, korar wasu manyan mambobi saboda zargin ayyukan da suka saba wa jam’iyya. Wadanda aka kora sun hada da Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike da sakataren jam’iyyar, Samuel Anyanwu da tsohon gwamnan Jihar Ekiti, Ayodele Fayose da mashawarcin shari’a na jam’iyya, Adeyemi Ajibade (SAN) da Umar Bature da AbdulRahman Mohammed da Mao Ohuambuwa da George Turner da Austin Nwachukwu da Abraham Ammah da kuma Dan Orbih.

Babban abin da taron ya kunsa shi ne zaben babban lauya daga Jihar Kebb, Kabiru Turaki a matsayin sabon shugaban jam’iyyar PDP. Sakatare taron, Sanata Ben Obi ya bayyana cewa Turaki ya samu kuri’u 1,516, wanda ya ba shi damar zama sabon shugaban PDP.

Haka kuma an zabi Mista Solarin Adekunle, a matsayin mataimakin sakataren tsare-tsaren al’amura na jam’iyyar, yayin da wasu ‘yan takara da dama suka sami dawowa mukamansu ba tare da hamayyar ba bayan janye ‘yan adawarsu.

A cikin jawabinsa na karbar mukami, Turaki ya ce ya fahimci girman nauyin da aka dora a wuyansa da na jagorantar kwamitin gudanarwa na jam’iyyar, yana mai kara cewa wajibi ne su cika aikin da aka dora musu ga ‘yan Nijeriya cikin aminci.

Ya bayyana cewa sabuwar shugabanci za ta fitar da ka’idojinta da tsarin aiki nan ba da jimawa ba, tare da jaddada cewa kwamitin zai fara aiki nan take. Yayin da yake jaddada cewa PDP ce kadai jam’iyyar siyasa a kasar da ta kiyaye asalinta tun farkon kafuwarta.

Ya ce, “Nauyin da kuka dora mana yana nufin cewa kuna kallo mu don mu kai ga ciki ga mutanen Nijeriya, kuma za mu yi haka. Ba mu yin tunanin karya cewa aikin da aka ba mu abu ne mai sauki. Jam’iyyarmu na cikin wani yanayi mai wahala yanzu, amma muna da karfin yin aikin da kuma karfin fuskantar kalubale.

“Ba da dadewa ba, za mu bayyana mene ne ka’idodinmu masu jagoranci da kuma yadda za mu cimma su. Lokacin da muke yin hakan, za mu fara aiki cikin sauri tun daga ranar farko. Yau, yayin da nake magana da ku, jam’iyyar siyasa daya tilo da ta ci gaba da rike sunanta ita ce jam’iyyar PDP. Wannan ya yiwu ne saboda wannan jam’iyya ce ta mutanen Nijeriya.”

Abin da ba a yi shakka a kai ba shi ne, babban taron ya gudana ne bisa saba wa hukuncin kotu da suka yi kokarin dakatar da shi, yayin da wakilai da masu jawabi daban-daban suka koma kan batun shari’o’in. Duk da haka, ga masu lura da siyasa, lokaci ne kawai zai nuna ko sakamakon zai taimaka wajen kawo karshen rikice-rikicen da ke damun jam’iyyar ko kuwa zai kara haddasa su.

PDP
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa
PDP
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
NDLEA Ta Cafke Mutane 230 Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

NDLEA Ta Cafke Mutane 230 Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.