ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC

by Yusuf Shuaibu
2 days ago
APC

Jam’iyyar hadaka ta ADC ta bayyana cewa sauyin sheka na gwamnonin da sauran ‘yan siyasar da aka zaba zuwa jam’iyyar APC ba zai iya tabbatar da tazarcen Shugaban kasa Bola Tinubu zuwa Aso Rock a zaben 2027 ba.

A yayin da yake yin hira ta musamman ga manema labarai a taron masu ruwa da tsaki na jam’iyya a ranar Asabar a Yola, shugaban jam’iyyar ADC reshen Jihar Adamawa, Shehu Yohanna, ya ce ‘yan siyasa da ke komawa jam’iyyar APC mai mulki suna shiga cikin bautar siyasa.

  • Wang Yi Ya Zanta Da Ministocin Wajen Cambodia Da Thailand 
  • Kifi Na Ganin Ka Mai Jar Koma!

Ya ce jam’iyyar ta riga ta yanke shawarar bai wa tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar takarar shugaban kasa, sannan Peter Obi a matsayin mataimakin dan takarar shugaban kasa a zaben 2027.

ADVERTISEMENT

“APC na jan ‘yan siyasa masu matukar bukata da marasa muhimmanci cikin jam’iyyarsu, suna neman jama’a marasa amfani da marasa muhimmanci wadanda ba su da amfani a lokacin zaben 2027.

“Gwamnonin da ke barin jam’iyyarsu zuwa APC su ne wadanda suka gaza matuka kuma suna kokarin dawowa don samun wa’adinsu na biyu.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama

NNPP Ta Buƙaci INEC Ta Yi Watsi Da Tarukan Jam’iyyar Da Kwankwaso Zai Jagoranta

“Sauran gwamnonin da suka sauya sheka da mambobin majalisar dokokin kasa sune wadanda ke kokarin tsere wa hukuncin hukumar yaki da cin hanci da rashawa. Ka tuna lokacin da tsohon shugaban jam’iyyar APC, Sanata Adams Oshiomhole, ya ce, ‘an yi maku gafara idan kuka shiga APC.

“Wannan na nufin sun rasa tasirin siyasa a cikin jam’iyyunsu da jihohinsu. Kuri’u ba sa tare gwamnonin, amma suna tare da talakawa,” in ji Yohanna.

Dangane da zaben cike gurbi na majalisar karamar hukumar Ganye, ya ce, “Zaben cike gurbin majalisar na karamar hukumar Ganye na nuni ga Shugaba Tinubu cewa ya tara mutane marasa amfani a APC. An tura jami’an tsaro sama da 6,000 zuwa Ganye tare da ministoci daga jihohi daban-daban, duk da haka APC ta samu nasara da kuri’u 96, wannan abin kunya ne.

“Idan a shekarar 2023 APC ta lashe wannan kujerar da kuri’u sama da 4,000 kuma a shekarar 2025 APC ta lashe da kuri’u 96 kawai, hakan na nufin jam’iyyar ta rasa tasirinta a Nijeriya,” in ji shi.

Yohanna ya bayyana cewa Atiku ne kawai dan takara da ke da karfin doke APC a zaben shugaban kasa na 2027.

“Manufofin gwamnatin yanzu na yin kamfen ne wajen kalubalantar dawowar Tinubu. Ta yaya za mu ci gaba idan gwamnati ta ce mutum daya zai iya cire kudi na naira 500,000 a mako daya kawai, kuma kungiyoyin kasuwanci su kuma naira 10,000,000 a mako? Tinubu ya jawo koma baya ga kasar nan,” in ji shi.

Ya yi kira ga mambobin ADC su yi rajistar katin zabe, yana cewa hakan shi ne mabudin cire Shugaba Tinubu daga ofis.

“Wadanda ke sa ran yin magudi a zaben 2027 za su ji kunya lokacin da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa ta fitar da sakamakon zabe,” in ji shi.

Yohanna ya yi kira ga ‘yan Nijeriya su kare kuri’unsu ta hayar da shari’a ta taada don amfanin dimokuradiyya, yana gargadin cewa tsarin jam’iyya guda zai sanya dimokuradiyya a cikin mawuyacin hali.

Bisa ga zaben kananan hukumomi na Jihar Adamawa, ya tabbatar wa mambobin jam’iyya cewa ADC za ta lashe dukkan kujerun shugabancin kananan hukumomi 21 da dukkan mazabun da ke jihar baki daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama

December 19, 2025
Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027
Tambarin Dimokuradiyya

NNPP Ta Buƙaci INEC Ta Yi Watsi Da Tarukan Jam’iyyar Da Kwankwaso Zai Jagoranta

November 28, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

PRP Ta Gargadi Sabon Shugaban PDP Kan Neman Taimakon Kasashen Waje A Rikicin Jam’iyya

November 28, 2025
Next Post
Sin Ta Bukaci Japan Da Ta Kauracewa Kalubalantar Ginshikin Dokar Kasa Da Kasa 

Sin Ta Bukaci Japan Da Ta Kauracewa Kalubalantar Ginshikin Dokar Kasa Da Kasa 

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025
Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.