ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PRP Ta Gargadi Sabon Shugaban PDP Kan Neman Taimakon Kasashen Waje A Rikicin Jam’iyya

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
9 months ago
PDP

Jam’iyyar PRP ta gargadi sabon shugaban PDP na kasa, Tanimu Turaki (SAN), da ya janye kalamusa na kiran Shugaban Amurka, Donald Trump, don tsoma baki a rikicin jam’iyyar.

A cikin wata sanarwa da shugaban PRP na kasa, Falalu Bello, ya fitar, ya bayyana kiran a matsayin rashin hankali da hadari kuma wanda bai dace da kasar ba.

  • Dabarun Sojoji Na Yaki Da Ta’addanci Ba Ya Aiki – Gwamnan Kebbi
  • Allah Ya Bai Wa Annabi (SAW) Mu’ujizozi Fiye Da 2,000 A Alƙur’ani

A yayin da yake magana da ‘yan jarida bayan samun shiga cikin hedikwatar jam’iyyar PDP a Abuja bayan dogon rikici tsakanin magoya bayan bangarorin adawa a ranar Talata, Turaki ya roki Shugaba Trump da ya tsoma baki a rikicin jam’iyyar.

ADVERTISEMENT

“Ina so in yi kira ga Shugaba Trump, abin da ke faruwa a yanzu ba kawai kisan kare dangi ba ne ga kiristocin Nijeriya har da ma dimokuradiyyar,” in ji Turaki.

Amma a martaninta, PRP ta ce irin wannan kalamai na matukar ruguza kasa tare da ci gaba da kawo rudani idan har shugabannin siyasa na furta irin wannan kalamai masu daci.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

Ta ce, “Wannan kalamai yana nuna wata matsala ta rashin amincewa da dorewar Nijeriya da ciiyoyin dimokuradiyya, ba tare da la’akari da yadda mutane suke kallonsu ba, da kuma karfin hadin kan mutanen kasar.

“Hakan cin zarafi ne ga ‘yancin kai, ‘yancin mallaka, da darajar Nijeriya tare da wulakanta dabi’u da dimbin ‘yan kasa masu kishin Nijeriya.

“Nijeriya kasa ce mai ‘yanci kuma an kafa ta a matsayin jamhuriya tare da iyakokin da aka ayyana, tana da gwamnati mai ‘yanci tare da tsoma bakin kowacce kasar waje ba.

“Muna kira ga Tanimu Turaki da PDP da su janye wannan furuci mai zafi da rashin fahimta nan take. Haka kuma, muna kira ga dukkan shugabannin Nijeriya da su kiyaye darajar kasarmu kuma su kaurace wa duk wani lamari da zai iya rage ikonmu ta hanyar neman taimako daga kasashen waje. Karfin Nijeriya yana cikin mutanenta, hukumominta, da kuma jajircewarta mara yankewa wajen gina kasa mai adalci da hadin kai.

“Dole ne a warware matsalolinmu ta hanyar tattaunawa ta cikin gida, hanyoyin dimokradiyya masu karfi, da jagoranci mai kishin kasa, ba ta hanyar karfi daga kasashen waje ba. Bai kamata a nemi taimakon kasashen waje ba a harkokin cikin gida don amfanin kashin kai,” in ji jam’iyyar.

PDP
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa
PDP
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Taya Murnar Kiran Taron Wakilan Gamayyar Kungiyoyin Masu Aikin Sa Kai Ta Kasar Sin Karo Na 3

Xi Jinping Ya Taya Murnar Kiran Taron Wakilan Gamayyar Kungiyoyin Masu Aikin Sa Kai Ta Kasar Sin Karo Na 3

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.