• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsananin Zafin Kaye A Zaɓen Fidda Gwani Yasa Wike Sambatu – Babba Mazoji

by Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
in Siyasa
0
Tsananin Zafin Kaye A Zaɓen Fidda Gwani Yasa Wike Sambatu – Babba Mazoji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk zantukan da ke futa daga bakin Mai girma Gwamnan Jihar Rivers Nelson Wike sambatu ne Kawai na Zafin Kaye da yasha a Zaɓen Fidda Gwani da aka gudanar a baya. Honarabul Zaharaddeen Babba Mazoji Tsohon Dan takarar kujerar Sanata a Shekara ta 2019 Kuma guda cikin Dattijan Jam’iyyar PDP a Jihar Katsina ne ya bayyana haka ga manema Labarai a Abuja.

Honarabul Zaharaddeen Babba Mazoji yace “na saurari tattaunawar da akayi dashi inda ya bayyana wasu maganganu da basu kamata ace sun fito daga bakin mutun irin Wike ba, Wanda mutum ne mai qima a wajena kasancewar ya bayar da gagarumar  gudunmawa a baya. Abin akwai mamaki Wanda tun kafin lokacin Zaɓen fidda Gwani lokacin wani taro da akayi a Legas mun bayar da shawara inda akayi watsi da bukatar nuna wani dan Takara daga wata shiyya wanda hakan baya cikin kudin tsarin mulkin Jam’iyyar PDP.

  • Da Gaske Atiku Ya Hakura Da Wike?

“Kuma Wike mantawa ya yi sune sukayi uwa kuma sukayi makarbiya wajen tabbatar da fitowar Shugaban Jam’iyyar PDP daga arewa domin a zatonsu shikenan sai Shugaban Kasa ya fito daga kudu? Sun manta wanca kudiri ko tattaunawa da akayi a Jihar Legas cewa Kujerar Shugaban Kasa ‘yace a ruwa ta mai rabo, an aminta duk Mai sha’awa ya fito ya tallata hajarsa. Kuma ai shi Wike dashi akayi takarar fidda  Gwani na Kujerar  Shugaban Kasa na Jam’iyyar PDP,  mai girma Alhaji Atiku Abubakar ya rangada shi da Kasa. Sannan ko a zantawar tasa ya tabbatar da cewa mulki Allah ke bada shi ga wanda yaso, shike nan Allah ya baiwa Atiku sai ciwon hassada ya bayyana? Inji Mazoji

Da aka tambayeshi kan matsayar Wike da ‘yan barandarsa kan Ficewa daga tawagar yakin neman zaɓen Atiku, Mazoji ya bayyana cewa wannan Shure shure ne da baya hana mutuwa,  abinda Wike ya kamata ya fahimta Kashi 90%  na masu zugashi wasu mutane ne da ko a akwatinsu ba zasu iya katabus ba, wasu kuma tsoffin Gwamnoni ne data kare masu suke dan lasar abin sawa a baka daga Gwmna Wike, Wanda Ina tabbatarwa da Wike cewa sauran ‘yan Kwanaki wa’adin mulkinsa ya kare duk guduwa zasu yi su barshi. Yanzu haka wani adadi mai yawa daga cikin masu rajin goya masa baya (Wike) duk sun tabbatar da Atiku suke, Idan Kuma  sun koma kusa dashi su nuna suna tare dashi.

Da aka tambayeshi baya ganin cikin jawaban Wike ya nuna yana cikin Jam’iyyar ta PDP kuma zai ci gaba da yakarta? Babba Mazoji cewa ya yi, mu Wike ba wata barazana bace ga takarar Wazirin Adamawa, domin duniya ta fahimci Wike da ‘yan korensa Arewa ce basa kauna, kuma ya kamata na tunawa Wike idan mantawa ya yi, ya manta Shekara nawa Obasanjo ya yi akan karagar mulki, Shekara Nawa Goodluck ya yi Kuma Shekara nawa Dattijon arziki Alhaji Musa ‘Yar Adua ya yi akan mulki, duka kusan Shekara Goma Sha Huɗu’ ‘yan kudu suka yi suna mulkar mu, kuma sai yanzu da Allah ya kawo lokacin Atiku hassada zata bayyana?

Labarai Masu Nasaba

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

Babba Mazoji ya tabbatarwa da masu irin wancan ciwon hassada cewa suyi hakuri mulki Allah ke ba dashi ga wanda yaso, yanzu kuma alamu sun bayyana Wazirin Adamawa Alhaji Atiku Abubakar shi ne Shugaban kasarmu na gobe da yardar Allah. Jama’ar Nijeriya Mun sha azaba a hannun Jam’iyyar APC, ga talauci, rashin tsaro, Yajin aikin Malaman Jami’a, Sayar da kadarorin Gwamnati, Jama’a duk sun zama mahaukata saboda tsananin yunwa, wannan tasa Jama’ar  Nijeriya yanzu sun gamsu Jam’iyyar PDP itace Jirgin fiton Al’umma.

A Karshe Babba Mazoji ya yiwa Jama’ar Kasarnan busharar kyawawan manufofin Atiku Abubakar, wanda zarar Allah ya bashi wannan dama aiwatarwa kawai za’a fara, ba kamar Gwamnatin APC ba data hau mulki babu wasu kwararan munufofin ciyar da Kasa gaba. Muna sanar da Jama’a sauran kwanki kadan ya rage a kaddamar da yakin neman zabe, wanda kowa zaiga irin fitar da zamuyi domin gaisawa da al’ummar Kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministan Wajen Kasar Sin Ya Halarci Taron Ministocin BRICS

Next Post

An Nada Sanatan PDP Cikin Kwamitin Yakin Zaben Tinubu

Related

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

2 days ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

3 days ago
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa
Siyasa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

6 days ago
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC
Siyasa

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

6 days ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Siyasa

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

1 week ago
2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

1 week ago
Next Post
An Nada Sanatan PDP Cikin Kwamitin Yakin Zaben Tinubu

An Nada Sanatan PDP Cikin Kwamitin Yakin Zaben Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

September 12, 2025
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

September 12, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

September 12, 2025
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

September 12, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.