• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Gaske Atiku Ya Hakura Da Wike?

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Da Gaske Atiku Ya Hakura Da Wike?

Atiku da Wike

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A daidai lokacin da rikicin jam’iyyar PDP ke ci gaba da ta’azzara, dan takarar shugaban kasa a karkashin tutar jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya ci gaba da shirye-shiryen zaben 2023 bayan ya kasa samun fahimtar juna da Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike.

Wannan na zuwa ne bayan samun rahotonin ganawar Gwamnan Ribas da takwarorinsa na jihohin Oyo da Benuwe da Abiya a Landan tare da dan takarar shugaban kasa, wadanda suka dage ba za su goyi bayan Atiku ba a karkashin jam’iyyar matukar aka kasa biya musu bukatocinsu.

  • Kashi 31 Na ‘Yan Nijeriya Ba Su Iya Karatu Da Rubutu Ba ― Gwamnatin Tarayya
  • Da Dumi-Dumi: Jami’an Tsaro Sun Kai Samame Gidan Tukur Mamu

Haka kuma rahotonnin sun bayyana cewa an samu ganawa tsakanin Wike da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu da ‘yan takaran gwamna na APC na jihohin Benuwe da Ribas da kuma Oyo.

Ana tsammanin majalisar zantarwa ta PDP za ta gudanar da taro a wannan mako domin tabbatar da yadda za a fara gudanar da yakin neman zaben shugaban kasa kafin ranar 28 ga watan Satumba.

An dai bayyana cewa jam’iyyar ta watsar da mafi yawancin shiryeshiryanta saboda zaman sulhu tsakanin Wike da Atiku.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

Wata majiya ta bayyana wa LEADERSHIP dalilan da ya sa shugaban jam’iyyar, Dakta Iyorchia Ayu ya bata wa Wike da wasu rai shi ne, Atiku zai hakura da Wike.

Ayu ya dage a kan ba zai taba sauka daga shugabancin jam’iyyar ba har sai ya cika wa’adin mulkinsa na shekaru hudu, wanda bangaren Wike suka bukaci ya sauka daga mukaminsa, inda ya kada baki ya ce lokacin da suka shiga jam’iyyar PDP a shekarar 1998, gwamnan Jihar Ribas yana yaro. Wike ya mayar wa Ayu martani wanda ya yi gargadin cewa zai taimaka wajen faduwar PDP a zaben 2023.

Majiyar ta kara da cewa Wike ne ya farfado da jam’iyyar PDP lokacin da jiga-jigan jam’iyyar suka kaurace mata a shekarar 2015, inda har ta dawo cikin hayyacinta.

A wannan makon ne, Atiku ya ganawar sirri da ‘yan takarar gwamna a karkashin jam’iyyar a dukkan jihohin kasar nan.

Atiku ya yi wannan ganawa ce tare da mataimakinsa, Gwamnan Jihar Delta, Ifeanyi Okowa a gidansa da ke Asokoro cikin garin Abuja.

A cikin wadada suka halarci ganawar sun hada da ‘yan takaran gwamna a jihohin Kaduna, Filato, Katsina, Legas, Neja, Kano, Sakkwato, Delta, Yobe, Jigawa, Nasarawa, Kwara, Benuwe, Borno, Ebonyi da kuma Zamfara.

Ganawar Atiku da ‘yan takarar ta zo ne bayan da shugabannin jam’iyyar suka bayyana tsarin gudanar da yakin neman zabe. A ganawarsa da ‘yan jarida a Abuja, sakataren jam’iyyar PDP, Hon Debo Ologunagba ya bayyana cewa jam’iyyar ba za ta taba rugujewa ba saboda wani mutum. “Wannan jam’iyyar tana martaba duk wani dan PDP.

Wike ya kasance babban barazana ga Nijeriya ba wai ga jam’iyyar PDP ba. PDP ba ta mutum daya ba ce.

“Dukkan bangarorin jam’iyyar suna aiki tare domin cimma muraduta. Dole mu amince da bukatun kowa saboda kar mu yi asarar sa. Muna tafiya da dukkan ra’ayoyin ‘ya’yan jam’iyyar.

“A hankali mun kusa cimma matsaya. Muna da bambancin ra’ayi, amma ba ma cikin rikici. Muna da rashin amincewa wajen zabi. Babu wata rikici a PDP, amma muna da bambancin ra’ayoyi wanda Dan’adam yake da shi a halittarsa.

“Dole sai mun hada kai za mu iya ceto jam’iyyar. Shugabannin da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar sun hada kansu wuri daya kan wannan lamari. Jam’iyyar za ta ci gaba da gudanar da shirye-shiryenta domin ceto kasar nan,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AtikuPDPRikiciSiyasaSulhuWike
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rayuwata A Shekara 70 -Mai Martaba Etsu Nupe

Next Post

“Akwai Matsala Game Da Bakin Da Ke Kwararowa Jihar Kano”

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 month ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
“Akwai Matsala Game Da Bakin Da Ke Kwararowa Jihar Kano”

“Akwai Matsala Game Da Bakin Da Ke Kwararowa Jihar Kano”

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

July 1, 2025
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

July 1, 2025
Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.