ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Gaske Atiku Ya Hakura Da Wike?

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Atiku da Wike

Atiku da Wike

A daidai lokacin da rikicin jam’iyyar PDP ke ci gaba da ta’azzara, dan takarar shugaban kasa a karkashin tutar jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya ci gaba da shirye-shiryen zaben 2023 bayan ya kasa samun fahimtar juna da Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike.

Wannan na zuwa ne bayan samun rahotonin ganawar Gwamnan Ribas da takwarorinsa na jihohin Oyo da Benuwe da Abiya a Landan tare da dan takarar shugaban kasa, wadanda suka dage ba za su goyi bayan Atiku ba a karkashin jam’iyyar matukar aka kasa biya musu bukatocinsu.

  • Kashi 31 Na ‘Yan Nijeriya Ba Su Iya Karatu Da Rubutu Ba ― Gwamnatin Tarayya
  • Da Dumi-Dumi: Jami’an Tsaro Sun Kai Samame Gidan Tukur Mamu

Haka kuma rahotonnin sun bayyana cewa an samu ganawa tsakanin Wike da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu da ‘yan takaran gwamna na APC na jihohin Benuwe da Ribas da kuma Oyo.

ADVERTISEMENT

Ana tsammanin majalisar zantarwa ta PDP za ta gudanar da taro a wannan mako domin tabbatar da yadda za a fara gudanar da yakin neman zaben shugaban kasa kafin ranar 28 ga watan Satumba.

An dai bayyana cewa jam’iyyar ta watsar da mafi yawancin shiryeshiryanta saboda zaman sulhu tsakanin Wike da Atiku.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

Wata majiya ta bayyana wa LEADERSHIP dalilan da ya sa shugaban jam’iyyar, Dakta Iyorchia Ayu ya bata wa Wike da wasu rai shi ne, Atiku zai hakura da Wike.

Ayu ya dage a kan ba zai taba sauka daga shugabancin jam’iyyar ba har sai ya cika wa’adin mulkinsa na shekaru hudu, wanda bangaren Wike suka bukaci ya sauka daga mukaminsa, inda ya kada baki ya ce lokacin da suka shiga jam’iyyar PDP a shekarar 1998, gwamnan Jihar Ribas yana yaro. Wike ya mayar wa Ayu martani wanda ya yi gargadin cewa zai taimaka wajen faduwar PDP a zaben 2023.

Majiyar ta kara da cewa Wike ne ya farfado da jam’iyyar PDP lokacin da jiga-jigan jam’iyyar suka kaurace mata a shekarar 2015, inda har ta dawo cikin hayyacinta.

A wannan makon ne, Atiku ya ganawar sirri da ‘yan takarar gwamna a karkashin jam’iyyar a dukkan jihohin kasar nan.

Atiku ya yi wannan ganawa ce tare da mataimakinsa, Gwamnan Jihar Delta, Ifeanyi Okowa a gidansa da ke Asokoro cikin garin Abuja.

A cikin wadada suka halarci ganawar sun hada da ‘yan takaran gwamna a jihohin Kaduna, Filato, Katsina, Legas, Neja, Kano, Sakkwato, Delta, Yobe, Jigawa, Nasarawa, Kwara, Benuwe, Borno, Ebonyi da kuma Zamfara.

Ganawar Atiku da ‘yan takarar ta zo ne bayan da shugabannin jam’iyyar suka bayyana tsarin gudanar da yakin neman zabe. A ganawarsa da ‘yan jarida a Abuja, sakataren jam’iyyar PDP, Hon Debo Ologunagba ya bayyana cewa jam’iyyar ba za ta taba rugujewa ba saboda wani mutum. “Wannan jam’iyyar tana martaba duk wani dan PDP.

Wike ya kasance babban barazana ga Nijeriya ba wai ga jam’iyyar PDP ba. PDP ba ta mutum daya ba ce.

“Dukkan bangarorin jam’iyyar suna aiki tare domin cimma muraduta. Dole mu amince da bukatun kowa saboda kar mu yi asarar sa. Muna tafiya da dukkan ra’ayoyin ‘ya’yan jam’iyyar.

“A hankali mun kusa cimma matsaya. Muna da bambancin ra’ayi, amma ba ma cikin rikici. Muna da rashin amincewa wajen zabi. Babu wata rikici a PDP, amma muna da bambancin ra’ayoyi wanda Dan’adam yake da shi a halittarsa.

“Dole sai mun hada kai za mu iya ceto jam’iyyar. Shugabannin da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar sun hada kansu wuri daya kan wannan lamari. Jam’iyyar za ta ci gaba da gudanar da shirye-shiryenta domin ceto kasar nan,” in ji shi.

Atiku
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
“Akwai Matsala Game Da Bakin Da Ke Kwararowa Jihar Kano”

“Akwai Matsala Game Da Bakin Da Ke Kwararowa Jihar Kano”

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.