• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: APC Ta Dage Ranar Fara Yakin Neman Zabenta

by Sadiq
3 years ago
APC

Kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC, ya dage fara yakin neman zaben da aka shirya kaddamarwa a ranar Laraba.

Darakta-Janar na kwamitin yakin neman zaben Tinubu da Shettima, kuma gwamnan Jihar Filato, Simon Lalong, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a yau Talata.

  • Masar Ta Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Na Gwaji A Makarantun Midil Na Kasar
  • An Nada Sanatan PDP Cikin Kwamitin Yakin Zaben Tinubu

A cewarsa, an yi hakan ne domin daidaita jadawalin lokaci da jadawalin ayyuka ne domin ya yi daidai da harkokin duk masu hannu a cikin yakin neman zaben don samun nasararsa.

A cewarsa, nan ba da jimawa ba za a sanar da sabon lokacin da za a fara yakin neman zaben jam’iyyar.

Sanarwar ta ce; “Tun da farko mun shirya tattaki da addu’o’in zaman lafiya a ranar Laraba, 28 ga watan Satumba, 2022, don fara yakin neman zaben shugaban kasa na 2023 a hukumance. Mun kuma sanar da cewa mambobin kwamitin yakin neman zaben sun kai rahoto hedikwatar yakin neman zaben a ranar domin karbar wasikun nadi.

LABARAI MASU NASABA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

“Duk da haka, saboda fadada jerin sunayen don samun karin masu ruwa da tsaki da bukatun cikin gida a APC, mun yanke shawarar daidaita jadawalin wadannan ayyuka domin tabbatar da cewa kowa yana cikin jirgin kafin a fara ayyukan a hukumance.

“Saboda haka, ayyukan da aka sanar a baya na ranar 28 ga Satumba ba za su ci gaba da kasancewa ba.

“A matsayinmu na jam’iyya mai mulki kuma mafi inganci a Nijeriya, mun fahimci sadaukarwa da fahimtar dimbin mambobinmu wadanda suka fi son sadaukar da kansu don wannan gagarumin aiki da ke gabanmu. Hakan kuma ya nuna irin tsananin soyayyar da ‘ya’yan jam’iyyar ke yi wa ’yan takararmu

“Za a sanar da sabon kwanan wata da jadawalin abubuwan da za su faru nan ba da jimawa ba”.

Idan ba a manta ba ranar 28 ga watan Satumba, 2022, ita ce ranar da hukumar zabe mai zaman kanta (INEC), ta ware ta ga jam’iyyu da ‘yan takara don fara yakin neman zabe a hukumance.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
Manyan Labarai

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Next Post
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Ajalin Mutane 23, Mutane 116,000 Sun Rasa Muhallansu A Benuwe

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Ajalin Mutane 23, Mutane 116,000 Sun Rasa Muhallansu A Benuwe

LABARAI MASU NASABA

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.