• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saraki Ga Gwamnoni Masu Barin Gado: Ku Guji Katsaladan A Mulkin Wadanda Suka Gaje Ku

by Bello Hamza
2 years ago
Saraki

Tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki, ya nemi gwamnoni masu barin gado su guji katsalandan a harkokin gudanar da mulki a jihohinsu yayin da suke barin gwamnati a karshen watan Mayu.

Saraki ya bayyana haka ne a taron bikin bankwana da aka shirya wa gwamnonin masu barin gado da masu kama mulki a Abuja, Saraki, wanda tsohon gwamnan Jihar Kwara ne, ya shawarci gwamnoni 18 masu barin gado su rungumi sabon rayuwar da za su fuskanta su kuma shirya bayar da gudummawarsu a bangarorin rayuwa da daban daban.

  • Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Soke Nasarar Zababben Gwamnan Jihar Abia, Alex Otti
  • Mutum 2 Sun Shiga Hannu Kan Kisan Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Amurka

A sakon fatan alhairi ga gwamnonin, , Saraki ya yaba musu a kan yadda suka bayar da gudumawar bunkasa jihohinsu, sai dai ya karfafa bukatar da su bar gwamnonin da za su gajesu su gudanar da nasu ayyukan ba tare da katsalandan ba.

Ya kara da cewa, “A yayin da kuka kasance ba gwamnoni ba, ku bar wadanda suka gaje ku su yi aikinsu. Ku koma ga iyanlanku, na tabbatar da cewa a halihn yanzu mata da yaranku da jikokinu na nan duk sun kokasa ku koma gida ku yi ta zumunci a tsakaninsu, ku shirya fuskantar wata rayuwa daban, ku yi tanadin kudadenku don kudaden ba za su rinka shigowa kamar da ba.”

Wani tsohon gwamnan Jihar Neja, Babangida Aliyu ya nemi sabbi da tsofaffin gwamnonin su muhimmantar da jin dadin al’umma a jihohinsu ba tare da nuna banbanci siyasa ba.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Ya yi gargadi a kan mulkin kama karya, ya ce, irin haka ba zai haifar da da mai ido ba.

“Sau da dama zaka ji wasu na cewa, wannan lokacinmu ne, kada ku yi irin wannan kuskuren, wani tsohon gwamman da ya yi irin wannan ikirarin a yanzu yana can yana yawo a titi.”

Aliyu ya kara da cewa, zamaka gwamna ba yana nufin kai ne ka fi ilimi ko nagarta ba, watakila ma kai ne na karshe a aji a lokacin da kuke karatu amma Allah ya daukaka ka a kan haka kada ku rungumi girman kai a harkokinku.”

Haka kuma tsohon gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo, ya nemi tsohofaffain gwamnoni su guji katsalanda a harkokin mulkin jihohin na su, su bar sabbin gwamnoni su yi aikin su ba tare da kawo musu cikas ba, ya nemi su rungumi wasu harkokin da za su taimaki rayuwar su.

Taron ya samu halartar manyan baki da dama, da suka hada da, Kayode Fayemi, Aminu Tambuwal, Aminu Masari, Charles Soludo, Bala Mohammed, Babagana Zulum, Dauda Lawal, Reb Fr Hyacinth Alia da sauransu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Amsa Tambayoyin Da Aka Yi Masa Kan Taron Kolin G7 A Hiroshima

Kasar Sin Ta Amsa Tambayoyin Da Aka Yi Masa Kan Taron Kolin G7 A Hiroshima

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.