• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsayin Jami’o’in Nijeriya A Ma’aunin Jami’o’in Duniya (Ra’ayinmu)

by Sulaiman
3 years ago
in Rahotonni
0
Matsayin Jami’o’in Nijeriya A Ma’aunin Jami’o’in Duniya (Ra’ayinmu)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fiye da wani lokaci, rahoton da aka fitar na matsayin jami’o’in Nijeriya a ma’aunin jami’o’i na duniya ya nuna cewa, wannan ne lokaci fiye da wani lokacin da ake bukatar a maida da hankali a kan halin da harkar ilimi ta ciki a kasar nan musamman ilimin jami’a a kasar nan.

Rahoton da Cibiyar ‘Times Higher Education’ ta fitar ya nuna cewa, gwarzuwar jami’a a Nijeriya ita ce, Jami’ar Afe Babalola (ABUAD) da ke Ado-Ekiti, wadda ta yi ta 400 a jerin jami’o’in duniya.

  • 2023: Kwankwaso Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Yi Watsi Da APC Da PDP

Cibiyar ta karbu a fadin duniya saboda sahihancin rahotannin da take fitarwa, cikin abubuwan da take lura dasu wajen yanke hukuncin zabar kwazon jami’a sun hada da abin da ya shafi bangaren karantarwa da bincike da kuma yadda jami’ar ta karbuwa a sassan duniya.

Yakamata a fahinci cewa, a shekarar 2022 cibiyar ta nazarci jami’o’i 1, 600 a kasashe 99. Cibiyar ta yi nazarin mukala fiye da Miliyan 108 da kuma kundin bincike da jami’o’i fiye da Miliyan 14.4 ta kuma karbi amsar tambayoyi daga masana fiye da 22,000 a fadin duniya.

Babu wata kasar Afrika data zo cikin jami’o’i na 100 na farko a jerin gwarazan jami’o’i duniya. Gwarzuwar jami’a data fi tsari a Afrika ita ce jami’ar kasar Afirka ta Kudu ‘Unibersity of Cape Town’ inda ta zo ta 183 a duniya. A Nijeriya kuma Jami’ar Ibadan da ta Legas suka zo na 401 da 501.

Labarai Masu Nasaba

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

A yayin da muke taya Jami’ar ABUAD murnar wannan nasarar, mun lura da cewa, wannan yana nuna irin tsananin yadda harkar ilimi ta tabarbarewar a kasar nan.

Duk da matukar muhimmancinta a wajen tafiyar da tattalin arzikin kasa gwamnatocin da suka gabata sun yi watsi da harkar ilimi, ta hanyar nakasa kasafin kudin da ake tanadar wa bangaren ilimin.

Akwai bukatar a sake nazarin kasafin kudin da jihohin kasar nan 36 ke samar wa bangaren ilimi musamman ma ganin kowacce jiha a halin yanzu ta mallaki jami’a ta kanta. Yayin da hukumar Majalisar Dinkin Duniya ta nemi a ware kashi 25 na kasafin kudin da aka kiyasta kashe ga bangaren ilimi har yanzu Nijeriya bata kai ga samar da kashi 15 ba.

A kasafin kudin shakarar 2022 gwmanatin Nijeriya ta ware wa bangaren ilimi Naira Tiriliyan 1.29 wanda ke nuna cewa kashi 7.9 kenan na kasasfin kudin da aka yi a shekarar. Wannan na nuna cewa an yi wa bangaren ilimi kashi 10 kenan duk kuwa da cewa, Majalisar Dinkin Duniya ta nemi ne aware kashi 25 na kasafin kudin a duk shekara don tallafa wa harkar ilimin al’umma.

Idan za a iya tunawa gwamnatin Buhari ta kasafta kashe Naira Tiriliyan 55.3 don gudanar da harkokin gwamnati a cikin shakara 6 na mulkinta amma Naira Tiriliyan 3.5 kawai aka ware wa bangaren ilimi wanda ke nuna kashin yana kasa da kashi 10, wanda ke nuna karara lamarin ilimi ba abin da gwamnatin ta dauka da muhimmanci bane.

Abin takaici a nan shi ne bangaren ilimi ya yi fama da matsalar kudade ga rashin kayan aiki da kuma karancin albashi ga kuma karancin ma’aikata wanda duk suna taimakawa wajen haifar da matsaloli ga bangaren ilimin tun daga firamare, sakandare har zuwa manyan makarantu.

Yawancin masana a bangaren ilimi basu yi mamakin ganin jami’o’in Nijeriya basu tabuka abin a zo a gani ba a tantancewa tare da matsayin su a tsakanin jami’o’in duniya, wannan yana faruwa ne saboda yawan yajin aikin da malaman jami’a ke shiga wanda ke haifar da cikas a abin da ya shafi bincike da karantarwa, fiye da wata 4 kenan malaman jami’o’i a Nijeriya ke yajin aiki har yanzu ba a kai ga warware matsalar ba.

A karkashin wannan gwamnatin kawai Malaman Jami’a sun yi yajin aiki na fiye da wata 13, wannan ba karamin asara ba ne ga harkar ilimi a Nijeriya.

Wadannan na daga cikin matsalolin da suka haifar da tabarbarewar ilimi a kasar nan kuma in har ba a magance su ba lamarin ilimi zai cigaba da tabarbarewa a kullum, hakan kuma abin kunya ne ga Nijeriya a idon duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

A Sansanin ‘Yan Hijira Na Jibiya: Mutum 15 Sun Mutu, An Haifi 35, Akalla Yara 3,000 Ba Su Karatu

Next Post

Sama Da Mutum 150 Ke Hannun ‘Yan Bindiga A Jibiya – Shugaban Karamar Hukumar

Related

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

1 day ago
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari
Rahotonni

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

4 days ago
Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa
Rahotonni

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa

2 weeks ago
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya
Rahotonni

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

2 weeks ago
Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda
Rahotonni

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

2 weeks ago
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

1 month ago
Next Post
Sama Da Mutum 150 Ke Hannun ‘Yan Bindiga A Jibiya – Shugaban Karamar Hukumar

Sama Da Mutum 150 Ke Hannun 'Yan Bindiga A Jibiya – Shugaban Karamar Hukumar

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.