• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zabar Mataimaki: Tinubu Ya Watsa Wa Gwamnonin Arewa Maso Yamma Kasa A Ido

by Sadiq
3 years ago
in Siyasa
0
Zabar Mataimaki: Tinubu Ya Watsa Wa Gwamnonin Arewa Maso Yamma Kasa A Ido
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Lahadi ne dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu ya zabi tsohon gwamnan jihar Borno, Kashim Shettima a matsayin wanda zai yi masa takarar mataimaki a zaben 2023.

Sai dai zabin nasa ya yi fami na gyambon ciwo ga wasu gwamnoni da mabiya a arewa maso yamma.

  • 2023: Ka Kula da Lafiyarka, Kwankwaso Ga Tinubu
  • Ku Kara Kaimi Wajen Inganta Tsaro – Buhari Ga Shugabanni Tsaro

Tun farko a jam’iyyar APC an shiga tsilla-tsilla kan wane ne ya fi dacewa ya yi wa Tinubu takarar mataimaki, lamarin da ya kai ga dan takarar daukar Kabiru Ibrahim Masari a matsayin mataimaki na wucin gadi.

Sai dai shi ma, Masarin ya yi murabus daga mukamin nasa gabanin bayyana daukar Shettima da Tinubu ya yi.

Sai dai wannan hukunci na Tinubu bai yi wa da dama dadi ba, ganin cewar suna da yakinin gwamnonin arewa maso yamma na muhimman mutanen da zasu iya cike masa wancan gibi.

Labarai Masu Nasaba

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

Wasu magoya baya na ganin cewar gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje na iya zama mataimakin Tinubu a zaben 2023, duba da irin gudunmawar da ya ba shi.

Wasu na ganin Ganduje yayi bajinta sosai tun farkon fara tafiyar Tinubu ta nuna son yi takarar shugaban kasa, inda suke da yakinin cewar gwamnan na Kano, na da gogewa da kuma duk abin da ake bukata sama da zabin na Tinubu (Shettima).

Wasu kuma na ganin cewar gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai, shi ne zabin da zai sa APC ta jijjiga jam’iyyar adawa ta PDP a babban zaben 2023.

Da fari wasu sun fara kiraye-kirayen da Tinubu ya dauki gwamnan na Kaduna, sai dai ba a san me ya faru aka haihu a ragaya ba.

A tunani irin na wadancan masu son Tinubu ya dauki El-Rufai, sun bayyana cewar gwamnan ya zama zakaran gwajin-dafi idan aka kwatanta shi da duk gwamnonin Nijeriya, wajen sanin salon shugabanci da kuma kware wajen sarrafa ayyukan ci gaba, musamman idan aka yi duba da yadda ya sauya fasalin birnin tarayya Abuja, lokacin da ya rike mukamin minista.

A wani kaulin kuwa, wasu masu sharhin siyasa na ganin Badaru Abubakar na jihar Jigawa, na iya zama mataimakin takarar Tinubu.

Wannan tunani nasu ba zai rasa nasaba da irin gudunmawar da a gwamnan na Jigawa ya bayar wajen farfado da jam’iyyar daga gargarar mutuwa a lokacin da ta ke fama da rikice-rikicen cikin gida ba.

Gwamnan na daga cikin mambobin kwamitin rikon kwarya na jam’iyyar karkashin jagorancin Mai Mala Buni.

Har ila yau, suna ganin janyewa Tinubu takarar shugaban kasa da gwamnan yayi a zaben fidda-gwanin APC, wannan ma wata alama ce da ke nuni da dacewar a zabe shi.

Sai dai duk da wannan kiraye-kiraye da wasu ke yi na zabar daya daga cikin gwamnonin na arewa maso yamma bai yi tasiri ba, domin kuwa Tinubu ya kunnen uwar shegu da su.

Tsohon gwamnan na Legas, ya zabi shugaban yakin neman zabensa na takarar shugaban kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2023BadaruEl-RufaiGandujeJigawaKadunakanoKashim ShettimaMataimakiTakarar Shugaban KasaTinubuZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 18 A Zamfara, Mutane Sun Tsere Daga Gidajensu

Next Post

Bukukuwan Babbar Sallah: Wane Tanadi Matasa Suka Yi?

Related

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

15 hours ago
Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
Da É—umi-É—uminsa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

2 days ago
Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

5 days ago
Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 
Siyasa

Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 

5 days ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

5 days ago
Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
Manyan Labarai

Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

5 days ago
Next Post
Bukukuwan Babbar Sallah: Wane Tanadi Matasa Suka Yi?

Bukukuwan Babbar Sallah: Wane Tanadi Matasa Suka Yi?

LABARAI MASU NASABA

aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Tinubu

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.