ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Rubutu A Kan Rayuwar Yau Da Kullum Domin Mutane Su Wa’azantu – Fatima Sunusi

by Sadiq
2 years ago
RUbutu

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

ADVERTISEMENT

Daya daga cikin hazikan marubutan littattafan Hausa na yanar gizo wato FATIMA SUNUSI RABI’U wacce aka fi sani da UMMU AFFAN, ta bayyana wa masu karatu dalilinta na fara rubutun littafin Hausa tare da irin nasarorin da ta samu game da rubutun, har ma da wasu batutuwan masu yawa. Ga dai tattaunawar tare da PRINCESS FATIMA ZARAH MAZADU kamar haka:

Ya sunan malamar?

To cikakken sunana shi ne; Fatima Sunusi Rabi’u, amma a ‘media’ an fi sani na da Ummu Affan.

Ko za ki fada wa masu karatu dan takaitaccen tarihinki?

An haife ni a shekarar Alif da dari tara da casa’in da bakwai (1997), a Jihar Katsina karamar hukumar Funtuwa. Na yi karatuna tun daga firamare zuwa karamar Sakandare a can, yayin da rayuwata ta dawo garin Kaduna anan na dora daga SS 1 har nayi kandi a 2015. Karatun addini ma Alhamdulillah nayi sauka sannan kuma ina da aure ma.

Me ya ja hankalinki har kika fara rubutu?

To gaskiya da farko sha’awa ce, domin tun ina karama nake sha’awar rubutu. Sannan na kasance makaranciyar littattafan Hausa hakan ne ma ya kara sa mini jin sha’awar rubutun har nake jin zan iya. Na kan sami littafi guda da biro na rubuta labari. A da, ina rubutawa na tara da niyyar watarana zan buga, kafin daga baya na ga ana rubutu a online ni ma na ce bari to na fara a nan.

Ya gwagwarmayar farawar ta kasance?

To Alhamdu lillahi ban sha wata wahala ba, kasancewar a midiya nake rubutun nawa, duk da dai da farko ni kadai nake fostin har daga baya kuma na ga wasu ma suna taya ni ba tare da na sani ba, to sai dai hamdala.

Ya batun iyaye lokacin da kika fara sanar musu kina son fara rubutu, shin kin samu wani kalubale daga gare su ko kuwa?

Ban fuskanci kalubale ba, don tun ina gida mahaifiyata na kara mini kwarin gwiwa. Shi ma mahaifina ban samu matsala da shi ba, ban sani ba ko dan sai da na yi aure sannan na fada masa ina rubutun tunda da ina gida ban buga ba sai bayan aurena na fara rubutu a Online.

Ya farkon fara rubutun ya kasance?

Gaskiya da farko ban sha wahala sosai ba, tun da ni ‘Online Writer’ ce, nakan yi rubutu ne kuma na tura, tun littafina na farko gaskiya Alhamdu lillah ya samu karbuwa sosai.

Kamar wanne bangare kika fi maida hankali akai wajen yin rubutu?

Ina rubutuna a kan rayuwar yau da kullum, fadakarwa, soyayya, nishadi da sauransu, maganar gaskiya babu inda bana tabawa indai na sami jigo to zan rubutu a kai domin masu irin abin su wa’azantu.

Kin rubuta labarai sun kai kamar guda nawa?

Eh! to gaskiya na rubuta labarai a kallah guda goma sha takwas 18, bayan gajerun labarai na shiga gasa da na dan rubuta a kalla bakwai.

Wanne labari ne ya zamo bakandamiyarki cikin wadanda ki ka rubuta?

Duka littattafaina ina kaunarsu kam, amma zan iya cewa ‘MU GANI A KASA…’ Yanzu shi ne bakandamiyata.

Wanne labari ne ya fi baki wahala wajen rubuta shi?

Littafina ‘SANDAR MAKAUNIYA’ kasancewar akwai siyasa a cikin labarin da tsaface-tsaface da kuma aljanu na dan sha wahala, musamman a kan aljanin da ke jikin yarinyar tun da ba jinsina ba ne, na dan sha wahala wajen ganin na rubuta abin da yake tamkar a zahiri.

Cikin labaran da ki ka rubuta ko akwai wanda ki ka buga?

Eh Alhamdu lillah akwai wata gasa da aka saka wani malaminmu ne a nan online na shiga cikin mutum biyar da aka buga wa labaransu, an buga mini BAKAR FURA… kuma ni ma na saka kudi aka kara yi min wasu, daga baya kuma na buga MU GANI A KASA… shi ma.

Za mu ci gaba mako mai zuwa

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)
Adabi

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

September 26, 2025
Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili
Adabi

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

April 19, 2025
Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa
Al'adu

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

December 30, 2024
Next Post
nauru

Ministan Harkokin Wajen Nauru: Dawo Da Huldar Diplomasiyya Tsakanin Sin Da Nauru Muhimmin Lokaci Ne A Tarihi

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.