• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

World Bank on glass building. Mirrored sky and city modern facade. Global capital, business, finance, economy, banking and money concept 3D rendering animation.

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya da Cibiyar Aikin Noma (IITA) da Bankin Duniya da kuma sauran masu ruwa da tsaki a fannin aikin no-ma, sun ayyana kudirinsu na yin hadaka mai karfi a kan aikin noma wanda ke tattare da fasahar zamani.

Sun ayyana yin hakan ne, domin kawo karshen matsalar rashin amfani da fasahar zamani a fadin wannan kasa da kuma Na-hiyar Afirka baki-daya.

  • ‘Yancin Kananan Hukumomi: Kotun Koli Ta Bai Wa Jihohi 36 Kwana 7 Su Kare Kansu
  • Rikicin Masarautar Kano: Lauyoyi Da Alƙalai Sun Tozarta Ɓangaren Shari’a – Shugaban Ƙungiyar Lauyoyi

Har ila yau, wannan kuduri na kunshe ne sakamakon wata ganawa da a aka yi tsakanin Mataimakin Shugaban Kasa, Sana-ta Kashim Shettima da wata tawaga da ta zo daga Cibiyar IITA da Bankin Duniya da kuma Cibiyar Gudanar da Bincken Tsarin Abinci ta Kasa da Kasa (IFPRI).

Kazalika, Mataimakin Shugaban Kasar; a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Stanley Nkwocha ya fitar ya ce; an yi wannan ganawa ce, a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja.

Jawabin Shettima a wajen ganawar ya bayyana cewa, shirin zai mayar da hankali ne kan yadda za a kara samar da wadataccen abinci a fadin kasar nan baki-daya.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Mataimakin ya ce, Cibiyar IITA ta kai matsayin da za ta taimaka wa ba Nijeriya kadai ba, har da ma dukkanin daukacin Nahiyar Afirka, ta yadda za a kara saita tsarin aikin noma da zai iya ju-rewa kowane irin sauyin yanayi tare da kara inganta Irin noma.

Haka zalika, ya yi nuni da cewa; Cibiyar IITA wadda aka kafa ta a shekarar 1967, ta jima tana bayar da gudunmawa ga wannan fanni na aikin noma a Nijeriya, sannan ya kara da cewa; har yanzu muna bukatar wannan gudunmawa tata.

Kazalika, Shettima ya sanar da cewa; nan da 2050, Nijeriya za ta kasance kasa ta uku cikin mafi yawan al’umma a doron kasa.

Ya sanar da cewa, Nahiyar Afirka na fusakantar kalubalen fari, sauyin yanayi da kuma kalubalen rashin tsaro, inda ya kara da cewa, fannin aikin noma na kasar nan na matukar fusakantar koma baya.
Har wa yau, Shettima ya yi kira ga Cibiyar ta IITA, da ta karfafa wannan hadaka, musamman domin samun damar zuba jari a fannin aikin noma ta fuskar kasuwanci.

Sannan kuma, ya bukaci cibiyar ta taimaka wa Nijeriya da ingantaccen Irin shuka na Masara da sauran amfanin gona, musamman Rogo.

Daga nan kuma, ya yaba wa IITA kan yunkurinta na samar da ingantaccen Irin Rogo a yankin kudu maso yamma, inda ya nemi cibiyar da ta kara fadada wannan shiri zuwa sauran kasashen da ke Nahiyar Afirka.
Tun da farko a nasa jawabin, Darakta Janar na Cibiyar IITA, Dakta Simeon Ehui, gode wa Shettima ya yi a kan shugabancinsa da kuma yadda ya mayar da hankali wajen bunkasa fannin aikin noma na kasar nan da kuma goyon bayan da yake bai wa cibiyar.

Dakta Ehui ya kara da cewa, tawagar ta zo Abuja ne; domin ganawa musamman a kan yadda za a sabunta yin hadaka da cibiyar da kuma sauran masu ruwa da tsaki, bisa nufin taimaka wa gwamnain tarayya na kokarinta wajen samar da wadatac-cen abinci a Nijeriya da kuma Nahiyar Afrika baki-daya.

Shi ma a nasa bangaren, Mataimakin Darakta Janar na IITA; Dakta Dashiell Kenton ya bayyana cewa, wannan cibiya tasu na taimaka wa wasu shirye-shiryen gwamnatin tarayya a fannin aikin noma, domin samar da damar kirkiro da wasu ayyukan yi, musamman ga matasan Nijeriya.

Haka zalika, ya yaba da fannin shirin noma don samun riba; wanda Gwamnatin Shugaban Kasa, Bola Tinubu ta kirkiro da shi, wanda ya yi nuni da cewa; shirin zai sake karfafa guiwar matasan kasar nan da dama.

Kazalika ya sanar da cewa, ta hanyar wannan shiri; cibiyar za ta tallafa wa manoman wannan kasa, musamman kanana ta hanyar ilimatar da su kan yadda za su bunkasa nomansu.

A nasa jawabin, Manajan Sashen Noma da Samar da Abinci na Bankin Duniya, Mista Abel Lufafa ya bayyana cewa, bankin da IITA da sauran masu hadaka; sun ji dadi da irin gudunmawar da Gwamnatin Shugaba Tinubu ke bayarwa, wajen kara habaka fannin aikin noma na Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AudugaManoman shinkafaNoman alkama
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masu Baje Kolin Kaya Kimanin 300 Za Su Halarci Bikin Kasuwancin Yammacin Afirka A Legas

Next Post

Manoma Za Su Amfana Da Tallafin Dala 25, 000 A Nasarawa

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

1 week ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

1 week ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

3 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

3 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

4 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

4 weeks ago
Next Post
bankin duniya

Manoma Za Su Amfana Da Tallafin Dala 25, 000 A Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

September 14, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Wani Sojan Gona Ɗauke Da Bindiga A Katsina

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

September 14, 2025
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

September 14, 2025
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

September 14, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.