• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Dage Shari’ar Matashin Da Ya Kone Masallata A Kano

by Sadiq
1 year ago
Kotu

Kotu ta dage shari’ar Shafiu Abubakar, wanda ake zargin ya yi sanadin mutuwar wasu masallata 19, a garin Gadan da ke karamar hukumar Gezawa a Jihar Kano. 

An dage zaman ne sakamakon rashin kara sunayen mutanen da suka mutu sakamakon lamarin.

  • Kenya Ta Dakatar Da Yi Wa Ma’aikatan Gwamnati Karin Albashi
  • JAMB Ta Bankaɗo Ɗalibai 3000 Da Suka Kammala Karatun Bogi

Leadership ta ruwaito cewar cewa, matashin mai shekaru 38, mazaunin kauyen Gadan da ke karamar hukumar Gezawa, na fuskantar shari’a a babbar kotun Kano da ke Rijiyar Zaki.

Tun da farko dai an zargi Abubakar da cinna wa wani masallaci wuta, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane 14 tare da raunata wasu da dama.

Sai dai mai gabatar da kara, karkashin jagorancin daraktan masu gabatar da kara (DPP) na ma’aikatar shari’a ta Jihar Kano, Barista Salisu Tahir, ya sanar da kotun cewa adadin wadanda suka mutu ya karu daga 14 zuwa 19 saboda haka ya bukaci karin lokaci don sabunta takardar tuhumar.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tahir ya ce “Muna neman wani kwanan wata don ba mu damar shigar da sabon sauyi don kara adadin wadanda abin ya shafa da kuma gabatar da shaidunmu a gaban kotu,” in ji Tahir.

A cewar masu gabatar da kara, Abubakar ya yi amfani da man fetur wajen cinna wa masallacin da ke kauyen Gadan wuta, a lokacin Sallar Asuba a ranar 15 ga watan Mayu, da misalin karfe 5:15 na asuba.

An garzaya da wadanda lamarin ya rutsa da au Asibitin Kwararru na Murtala Muhammad da ke Kano.

A cewar mai gabatar da karar, laifin ya saba da sashe na 336, 247, da 221 na dokar shari’a ta Jihar Kano.

Lauyar da ke kare wanda ake tuhuma, Barista Asiya Muhammad Imam, ta bukaci masu gabatar da kara da su gabatar da sabbin tuhume-tuhumen.

Daga bisani alkalin kotu, shari’a, Malam Halhalatul Huza’i Zakariyya, ya dage shari’ar zuwa ranar 18 da 19 ga watan Yuli, domin ci gaba da sauraren karar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima
Manyan Labarai

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Vladimir Putin

Xi Jinping Ya Gana Da Vladimir Putin

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.