• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministar Jin Kai Ta Raba Wa Mata 3,500 Tallafin Kudi A Gombe

by Najib Sani a Gombe
3 years ago
in Kananan Labarai
0
Ministar Jin Kai Ta Raba Wa Mata 3,500 Tallafin Kudi A Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministar jin kai da walwalar al’umma, Sadiya Farouk, a ranar Talata ta kaddamar da rabon tallafin kudi ga mata sama da 3,500 a jihar Gombe.

Ministar ta bada tallafin ne karkashin shirin taimakon mutane da suke fama da matsanancin talauci da ake wa lakabi ‘Conditional Cash Transfer’ (CCT) a turance.

  • NBC Ta Ci Tarar Trust TV Tarar Miliyan 5 Kan Yada Ayyukan ‘Yan Bindiga 
  • An Harbe Dogarin Mataimakin Sufeton ‘Yansanda Yayin Wani Harin ‘Yan Bindiga A Kaduna

Da take jawabi a yayin kaddamar da rabon kudin tallafin a babban zauren taro na gidan gwamnatin Gombe, ministar ta bayyana cewa wadanda aka zaba don cin gajiyar tallafin za su karbi Naira 20,000 kowannensu.

A cewarta, shirin tallafin na CCT na daya daga cikin abubuwan da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kirkiro karkashin tsarin rage talauci da inganta walwalar al’ummar kasa, wanda yake mika taimako ga mutanen da suka fi fama da talauci musamman a yankunan karkara.

Ta yi ikirarin cewa gwamnatin Buhari ta gaji talauci wajen kaso saba’in daga gwamnatocin baya, shi yasa ta mayar da hankali wajen samar da hanyoyin rage wahalhalun jama’a.

Labarai Masu Nasaba

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

“Wannan shirin yana daga wadanda suka fi ko wanne tasiri a nahiyar Afrika wajen rage fatara a tsakanin al’umma da kuma janyo hadaka daga kasashen duniya don inganta rayuwar al’umma”. Inji ministar.

Sadiya ta kara da cewa ita da kanta ta ga mutanen da a baya suke cikin mawuyacin hali amma yanzu sun canza sakamakon wannan tallafin da aka basu a sassa daban-daban na kasar nan.

Shi ma da yake jawabi, gwamnan jihar Gombe, Inuwa Yahaya wanda mataimakin gwamnan, Manasseh Jatau, ya wakilce shi ya yaba wa gwamnatin tarayya bisa tallafin yana mai cewa tallafin zai kara wa wadanda suka ci gajiyarsa hanyoyin samun kudin shiga.

Ya kuma shawarci wadanda suka karbi tallafin da su yi amfani da kudin a kasuwanci da sana’oi da za su janyo musu riba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FataraGombeGwamnatin TarayyaMataMinistar AgajiRage TalauciSadiya Umar FaroulTallafi
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makarantar Tarayya, Sun Kashe Mahaifin Wakilin NAN A Kaduna 

Next Post

Ana Zaton Wuta A Makera…

Related

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa
Kananan Labarai

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

2 months ago
Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

4 months ago
Ƙarin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arziƙin Duniya
Kananan Labarai

Ƙarin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arziƙin Duniya

4 months ago
Gwamnati Ta Amince Da Bai Wa Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Lasisi
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Amince Da Bai Wa Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Lasisi

5 months ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Kananan Labarai

Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Dala Tiriliyan 7 A Tsarin Kasuwancin Musulunci Na Duniya

11 months ago
Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Aikin Sake Gina Asibitin Talata Mafara
Labarai

Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Aikin Sake Gina Asibitin Talata Mafara

11 months ago
Next Post
Ana Zaton Wuta A Makera…

Ana Zaton Wuta A Makera...

LABARAI MASU NASABA

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

August 4, 2025
Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

August 4, 2025
Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

August 4, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara

August 4, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

August 4, 2025
Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

August 4, 2025
Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 

Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.