• English
  • Business News
Tuesday, July 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Suka Biyo Bayan Murabus Din Babban Jojin Nijeriya Ibrahim Tanko

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Rahotonni
0
Zargin Cin Hanci: Alkalin Alkalai, Tanko Muhammad Ya Ajiye Mukaminsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Litinin din makon jiya ne Alkalin-Alkalan Nijeriya, Justice Ibrahim Tanko Muhammad ya yi murabus na radin kashin kai bisa hujjojin rashin lafiya da ya bayar.

Shi dai Justice Tanko a watan Janairun shekarar 2019 ne shugaban kasa Muhammadu Buhari ya rantsar da shi a matsayin mukaddashin Alkalin Alkalan Nijeriya bayan dakatar da Alkalin Alkalan wancan lokaci, Walter Onnoghen kan zargin da aka masa na kin bayyana kadarorin da ya mallaka a rayuwarsa.

  • Yadda Aka Tilastawa Tsohon Alkalin-alkalai Tanko Yin Murabus Din Dole

Wannan matakin na murabus din Tanko na zuwa bayan da wasu manyan Alkalan Nijeriya su 14 suka yi ta korafin rashin samun ababen more rayuka da yanayin aiki mai inganci a karkashin jagorancin Justice Tanko, kodayake daga baya ya fito ya musu bayani dalla-dallah na dalilan da suka sanya wasu abubuwan da suke bukata bai samuwa.

Bayanai sun nuna cewa Mai Shari’a Olukayode Ariwoola shi ne alkali mafi girman mukami bayan murabus din mai Shari’a Ibrahim Tanko Muhammad, wanda kuma tunin shugaban kasa ya rantsar da shi.

A kan wannan kokarin nasa, shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya karrama shi da lambar karamci ta kasa ta GCON.
Buhari a lokacin da ke rantsar da sabon babban jojin Nijeriya, Justice Olukayode Ariwoola a matsayin wanda ya gaji Tanko Muhammad.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

Shugaban kasa ya jawo hankalin sashin shari’a da su kara azama a fagen aiki domin kada ‘yan Nijeriya su yanke kauna da fata daga garesu.

Shugaban kasan ya jinjina wa Tanko bisa irin nasarorin da ya iya cimmawa, don haka ne ya karramashi da lambar yabo ta GCON don nuna godiya da irin kokarinsa ga Nijeriya.

“Na amshi wasika daga wajen Honorabul Justice Dakta I. Tanko Muhammad CFR, na murabus dinsa a matsayin Alkalin Alkalan Nijeriya kuma shugaban majalisar shari’a ta Nijeriya bisa dalilai na rashin lafiya. Kuma murabus dinsa ta fara aiki nan take ne.

“CJN Tanko an nada a kotun daukaka kara a 2006, aka kuma rantsar da shi a ranar 8 ga watan Janairun 2007, ya zama babban Alkalin Nijeriya a matsayin mai rikon kwarya a ranar 25 ga watan Janairun 2019.

“An kuma rantsar da shi ya zama Alkalin Alkalai a ranar Laraba 24 ga watan July na 2019.” A cewar shugaban kasar, bisa yadda yake a tsare, tsohon CJN din ya kamata ne ya yi ritaya a ranar 31 ga watan Disamban 2023, amma bisa rashin lafiya ya amince ya ajiye aikin nasa.
Shugaba Buhari ya ce, sashin shari’a a karkashin jagorancin Tanko Muhammad an samu cimma nasarori masu tarin yawa da suka hada da yanke hukunci masu tarin yawa da tsare-tsaren da kotun daukaka kara ta samar, da kuma kara samar da wasu kotuna da kundin tsarin mulki ya samar, gami da yin aiki tukuru wajen bada hukunci ba tare da nuna son kai ko nuna bangaranci ba.

A cewar shugaban, tarihi ba zai mance da irin gudunmawar da Justice Muhammad ya baiwa sashin shari’a a Nijeriya ba, kyautata demoradiyya da cigaban kasa. Ya ce, a kan hakan ne suka duba dacewar bashi lambar yabo ta GCON.

Kazalika, shugaban ya bada tabbacin gwamnatinsa na cigaba da sake mara wa sashin shari’a a matsayin mai cin kashin kanta domin wanzar da adalci a kowani lokaci.

A jawabinsa bayan shan rantsuwa, sabon Alkalin Alkalan, Justice Ariwoola ya bai wa ‘yan Nijeriya tabbacin cewa ba zai taba watsa musu kasa a ido ba, zai yi iya kokarinsa wajen kyautata aiki domin lamura su dawo yadda suke.

Mukaddashin Alkalin Alkalan ya ce, “Abun da muke tsammani daga wajen ‘yan Nijeriya kawai su kasance masu bin dokoki da kwansitushin din kasa.”
Ya kuma ce babu wata baraka a sashin shari’a don haka ne yake mai tabbatar da cewa aiki zai inganta kuma jin dadi da walwalar alkalai zai kara samun tagomashi a karkashin jagorancinsa.
A gefe guda, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya yi fatan alkairi wa Justice Tanko Muhammad, ya kuma jinjina masa biya gudunmawar da baya bayar wa Nijeriya.
Sai ya jawo hankalin sabon mukaddashin CJN da ya yi amfani da gogewarsa wajen tafiyar da ayyukansa bisa tsarin doka da bin kwansitushin na kasa domin daurewar lamura da tafiyar da komai bisa gaskiya da adalci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Muhammad Abacha Ne Dan Takarar PDP A Kano- INEC

Next Post

2023: Kuri’un ‘Yan Nijeriya Ne Za Su Yanke Hukuncin Lashe Zabe – INEC

Related

Fyade
Rahotonni

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

3 days ago
APC
Manyan Labarai

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

3 days ago
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari
Labarai

Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

1 week ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

1 week ago
2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu
Manyan Labarai

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

1 week ago
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
Rahotonni

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2 weeks ago
Next Post
Sharhi: Ko INEC Za Ta Samu Nasarar Sahihin Zabe A 2023?

2023: Kuri’un ‘Yan Nijeriya Ne Za Su Yanke Hukuncin Lashe Zabe – INEC

LABARAI MASU NASABA

Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo

Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo

July 22, 2025
Ban Tsani Buhari Ba, Ina Sukar Sa Ne Kawai Kan Matsalar Tsaro – Ortom

Ban Tsani Buhari Ba, Ina Sukar Sa Ne Kawai Kan Matsalar Tsaro – Ortom

July 22, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

July 22, 2025
Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

July 22, 2025
Kasar Sin Na Fatan EU Za Ta Yi Aiki Da Ita Bisa Alkibla Guda Da Tsara Hadin Gwiwa Na Shekaru 50 Masu Zuwa

Kasar Sin Na Fatan EU Za Ta Yi Aiki Da Ita Bisa Alkibla Guda Da Tsara Hadin Gwiwa Na Shekaru 50 Masu Zuwa

July 21, 2025
PSC Ta Amince Da Ɗaga Darajar Jami’an ‘Yan Sanda 12 Daga Matakin CP Zuwa AIG, Da Sauransu

PSC Ta Amince Da Ɗaga Darajar Jami’an ‘Yan Sanda 12 Daga Matakin CP Zuwa AIG, Da Sauransu

July 21, 2025
Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba

Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba

July 21, 2025
Shirin Ba Da Horo A Kasar Sin Ya Taimaka Wa Inganta Masana’antar Gyadar Senegal

Shirin Ba Da Horo A Kasar Sin Ya Taimaka Wa Inganta Masana’antar Gyadar Senegal

July 21, 2025
Ana Iya Samun Masu Samar Da Kayayyaki Iri-Iri Cikin Awa Daya A Kasar Sin

Ana Iya Samun Masu Samar Da Kayayyaki Iri-Iri Cikin Awa Daya A Kasar Sin

July 21, 2025
Kotu Ta Kori Ƙarar Da APC Ta Shigar Kan Dakatar Da Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomin Kano

Kotu Ta Kori Ƙarar Da APC Ta Shigar Kan Dakatar Da Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomin Kano

July 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.