ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Suka Biyo Bayan Murabus Din Babban Jojin Nijeriya Ibrahim Tanko

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Tanko

A ranar Litinin din makon jiya ne Alkalin-Alkalan Nijeriya, Justice Ibrahim Tanko Muhammad ya yi murabus na radin kashin kai bisa hujjojin rashin lafiya da ya bayar.

Shi dai Justice Tanko a watan Janairun shekarar 2019 ne shugaban kasa Muhammadu Buhari ya rantsar da shi a matsayin mukaddashin Alkalin Alkalan Nijeriya bayan dakatar da Alkalin Alkalan wancan lokaci, Walter Onnoghen kan zargin da aka masa na kin bayyana kadarorin da ya mallaka a rayuwarsa.

  • Yadda Aka Tilastawa Tsohon Alkalin-alkalai Tanko Yin Murabus Din Dole

Wannan matakin na murabus din Tanko na zuwa bayan da wasu manyan Alkalan Nijeriya su 14 suka yi ta korafin rashin samun ababen more rayuka da yanayin aiki mai inganci a karkashin jagorancin Justice Tanko, kodayake daga baya ya fito ya musu bayani dalla-dallah na dalilan da suka sanya wasu abubuwan da suke bukata bai samuwa.

ADVERTISEMENT

Bayanai sun nuna cewa Mai Shari’a Olukayode Ariwoola shi ne alkali mafi girman mukami bayan murabus din mai Shari’a Ibrahim Tanko Muhammad, wanda kuma tunin shugaban kasa ya rantsar da shi.

A kan wannan kokarin nasa, shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya karrama shi da lambar karamci ta kasa ta GCON.
Buhari a lokacin da ke rantsar da sabon babban jojin Nijeriya, Justice Olukayode Ariwoola a matsayin wanda ya gaji Tanko Muhammad.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

Shugaban kasa ya jawo hankalin sashin shari’a da su kara azama a fagen aiki domin kada ‘yan Nijeriya su yanke kauna da fata daga garesu.

Shugaban kasan ya jinjina wa Tanko bisa irin nasarorin da ya iya cimmawa, don haka ne ya karramashi da lambar yabo ta GCON don nuna godiya da irin kokarinsa ga Nijeriya.

“Na amshi wasika daga wajen Honorabul Justice Dakta I. Tanko Muhammad CFR, na murabus dinsa a matsayin Alkalin Alkalan Nijeriya kuma shugaban majalisar shari’a ta Nijeriya bisa dalilai na rashin lafiya. Kuma murabus dinsa ta fara aiki nan take ne.

“CJN Tanko an nada a kotun daukaka kara a 2006, aka kuma rantsar da shi a ranar 8 ga watan Janairun 2007, ya zama babban Alkalin Nijeriya a matsayin mai rikon kwarya a ranar 25 ga watan Janairun 2019.

“An kuma rantsar da shi ya zama Alkalin Alkalai a ranar Laraba 24 ga watan July na 2019.” A cewar shugaban kasar, bisa yadda yake a tsare, tsohon CJN din ya kamata ne ya yi ritaya a ranar 31 ga watan Disamban 2023, amma bisa rashin lafiya ya amince ya ajiye aikin nasa.
Shugaba Buhari ya ce, sashin shari’a a karkashin jagorancin Tanko Muhammad an samu cimma nasarori masu tarin yawa da suka hada da yanke hukunci masu tarin yawa da tsare-tsaren da kotun daukaka kara ta samar, da kuma kara samar da wasu kotuna da kundin tsarin mulki ya samar, gami da yin aiki tukuru wajen bada hukunci ba tare da nuna son kai ko nuna bangaranci ba.

A cewar shugaban, tarihi ba zai mance da irin gudunmawar da Justice Muhammad ya baiwa sashin shari’a a Nijeriya ba, kyautata demoradiyya da cigaban kasa. Ya ce, a kan hakan ne suka duba dacewar bashi lambar yabo ta GCON.

Kazalika, shugaban ya bada tabbacin gwamnatinsa na cigaba da sake mara wa sashin shari’a a matsayin mai cin kashin kanta domin wanzar da adalci a kowani lokaci.

A jawabinsa bayan shan rantsuwa, sabon Alkalin Alkalan, Justice Ariwoola ya bai wa ‘yan Nijeriya tabbacin cewa ba zai taba watsa musu kasa a ido ba, zai yi iya kokarinsa wajen kyautata aiki domin lamura su dawo yadda suke.

Mukaddashin Alkalin Alkalan ya ce, “Abun da muke tsammani daga wajen ‘yan Nijeriya kawai su kasance masu bin dokoki da kwansitushin din kasa.”
Ya kuma ce babu wata baraka a sashin shari’a don haka ne yake mai tabbatar da cewa aiki zai inganta kuma jin dadi da walwalar alkalai zai kara samun tagomashi a karkashin jagorancinsa.
A gefe guda, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya yi fatan alkairi wa Justice Tanko Muhammad, ya kuma jinjina masa biya gudunmawar da baya bayar wa Nijeriya.
Sai ya jawo hankalin sabon mukaddashin CJN da ya yi amfani da gogewarsa wajen tafiyar da ayyukansa bisa tsarin doka da bin kwansitushin na kasa domin daurewar lamura da tafiyar da komai bisa gaskiya da adalci.

Tanko
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
Sharhi: Ko INEC Za Ta Samu Nasarar Sahihin Zabe A 2023?

2023: Kuri’un ‘Yan Nijeriya Ne Za Su Yanke Hukuncin Lashe Zabe – INEC

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.