• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Kula Ga Masu Cutar Siga

by Idris Aliyu Daudawa
3 years ago
in Rahotonni
0
Abubuwan Kula Ga Masu Cutar Siga
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ciwon Siga wata cuta ce dake da matukar hadari wadda ake kamuwa da ita lokacin da Pancrease wanda wani wuri a kusa da ciki wanda yake samar da sinadarin ‘INSULIN’ da kuma ruwan da yake taimakawa jiki narkar da abinci, ya kasance bai iya samar da sinadarin insulin,ko kuma lokacin da jiki ba zai iya yin amfani da shi.

Har yanzu ita ce cuta da take bada babbar matsala a karni na ashirin da daya, hakan ya kasance ne saboda matsalolin cututtukan da ake kamuwa da su.

  • 2023: Gwamnatinmu Za Ta Farfaɗo Da Harkar ilimi Da Walwalar Malamai – Atiku
  • LP, Ta Kori Daraktan Yakin Neman Zaben Obi, Okupe Da Wasu 11 Kan Gaza Biyan Harajin Jam’iyyar

Shugabar kwamitin amintattu ta wayar da kan al’umma wajen kokarin da ake yi na yakar cutar Dokta Afoke Isiabwe ta bayyana cewa cutar Siga ta shafi mutane kusan milyan 537 da kuma yara fiye da milyan 1.1 a fadin duniya wannan ya hada da ‘yan Nijeriya milyan ko wacce shekara.

Duk shekara cutar Siga tana kashe mutane kusan milyan hudu a duniya, ta dai kara jaddada cewa cutar tana iya shafar gaba daya ko wanne sashe na jiki.

Tana sanadiyar rashin gani na idanu, ga matsala mai shafar hakora, tsayawar aikin koda, cardiobascular disease, yanke hannu ko kafa, haduwa da matsala lokacin saduwa da mace, wannan sai idan ba a dauki matakan da suka dace ba.

Labarai Masu Nasaba

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

Tace yawancin abubuwan da cutar siga ta 2 ana iya maganinsu ta hanyar tafiyar da rayuwa yadda ta dace.

Ta bayyana alamun jan kunne na kamuwa da cutar siga da suka hada da lokacin da mutum yake fama jin kishirwa ko shan ruwa,har abin ya wuce kima, ga kuma yawan fitsari, jiki ya kasance babu nauyi saurin jin gajiya ko ba wata laka.

Mutum ya kasance cikin damuwa ko ya kasance a wani sauyin yanayi, ba zai iya gani sosai ba, idan ya yi rauni ba zai bai warkewa, yasai kuma ta bayyana har ila yau alamu na an kamu, lokacin da mutum yake jin ya kamu da cuta, kamar cutar dasashi, fata da cututtukan Farji da dai sauransu.

Bugu da kari tace yakamata ‘yan Nijeriya da akwai sauran hanyoyin da ake kamuwa da cutar kamar tarihin iyali dangane da cutar siga, yin kiba ko nauyin da ya wuce misali,cin abincin da bai dace ba, rashin motsa jiki, karuwar shekaru, hawan jini, amfani da abincin da bai kamata lokacin da mace take da juna biyu.

Har ila yau da akwai:glucose da tarihin ciwon sukari na ciki suna da alaka da nau’in ciwon sukari na 2, nau’in ciwon siga na 2 wanda shi ne wanda aka fi sani, uwa uba kuma ga tarihin cutar sigar mata masu juna biyu kan kamu da ita.

“Da akwai bukatar kowa ya lura da su wadannan alamun na cutar siga, domin a samu daukar matakain daya kamata saboda san yadda za a kula da cutar da hanyoyin kauce ma kamuwa da ita,bare ma har ma ta kai ga yin kamari.

“Hakanan ma mutane da sduka riga siuka kamu da cutar siga suna da bukatar taimako daga ‘yan’uwansu domin su iya tafiyarda yawan kudaden da ake kashewa wajen kokarin rabuwa da ita, sai kuma irin kallon da za a rika yi masu da su kuma yadda za su ji a jikinsu sanadiyar kamwa da cutar sikari.

Akwai bukatar a rika cin abincin da ya dace musamman ma mai gina jiki, da ci gaba da yawan motsa jiki, ga kuma lura da kada a bari nauyin jiki yayi yawan daya wuce misali.Ana iya duk tafiyar da duk matakan matukar ko wadanne iyalai za su lura da kuma yin amfani da matakan.”

Ta yi kira da ‘yan Nijeriya su san abubbuwan da suka kamata su sani danagane da cutar siga, da hanyoyin kauce ma kamuwa da ita, da mace- macen da ake yi snadiyar cutar.

Wayar da kan al’umma shi ne babban mataki saboda mutanen da suke fama da cutar, da kuma wadanda aka gwada sun kamu da ita amma basu san hanyar da za su bi ba wajen neman maganinta.

Daga karshe Isiabwe tayi kira da gwamnatoci sai masu kula da lafiyar al’umma da masu ruwa da tsaki, su kara zage damtse wajen samar da hanyoyin wayar da kan al’umma yadda za su fahimci al’amarin, hakan zai taimaka masu wajen lura da alamun kamuwa da cutar, da matakan da suka dace na rabuwa ko warkewa daga cutar siga.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CiwoKulaSiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Nijeriya Su Shirya Fuskantar Wahalar Rayuwa A 2023 – Sanata Yusuf

Next Post

Dalibin Da Ya Tsokani Aisha, Zai Gana Da Buhari A Villa

Related

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

7 hours ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

6 days ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

6 days ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

2 weeks ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

2 months ago
Next Post
Dalibin Da Ya Tsokani Aisha, Zai Gana Da Buhari A Villa

Dalibin Da Ya Tsokani Aisha, Zai Gana Da Buhari A Villa

LABARAI MASU NASABA

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

June 6, 2025
Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.