ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Kula Ga Masu Cutar Siga

by Idris Aliyu Daudawa
4 years ago
Siga

Ciwon Siga wata cuta ce dake da matukar hadari wadda ake kamuwa da ita lokacin da Pancrease wanda wani wuri a kusa da ciki wanda yake samar da sinadarin ‘INSULIN’ da kuma ruwan da yake taimakawa jiki narkar da abinci, ya kasance bai iya samar da sinadarin insulin,ko kuma lokacin da jiki ba zai iya yin amfani da shi.

Har yanzu ita ce cuta da take bada babbar matsala a karni na ashirin da daya, hakan ya kasance ne saboda matsalolin cututtukan da ake kamuwa da su.

  • 2023: Gwamnatinmu Za Ta Farfaɗo Da Harkar ilimi Da Walwalar Malamai – Atiku
  • LP, Ta Kori Daraktan Yakin Neman Zaben Obi, Okupe Da Wasu 11 Kan Gaza Biyan Harajin Jam’iyyar

Shugabar kwamitin amintattu ta wayar da kan al’umma wajen kokarin da ake yi na yakar cutar Dokta Afoke Isiabwe ta bayyana cewa cutar Siga ta shafi mutane kusan milyan 537 da kuma yara fiye da milyan 1.1 a fadin duniya wannan ya hada da ‘yan Nijeriya milyan ko wacce shekara.

ADVERTISEMENT

Duk shekara cutar Siga tana kashe mutane kusan milyan hudu a duniya, ta dai kara jaddada cewa cutar tana iya shafar gaba daya ko wanne sashe na jiki.

Tana sanadiyar rashin gani na idanu, ga matsala mai shafar hakora, tsayawar aikin koda, cardiobascular disease, yanke hannu ko kafa, haduwa da matsala lokacin saduwa da mace, wannan sai idan ba a dauki matakan da suka dace ba.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

Tace yawancin abubuwan da cutar siga ta 2 ana iya maganinsu ta hanyar tafiyar da rayuwa yadda ta dace.

Ta bayyana alamun jan kunne na kamuwa da cutar siga da suka hada da lokacin da mutum yake fama jin kishirwa ko shan ruwa,har abin ya wuce kima, ga kuma yawan fitsari, jiki ya kasance babu nauyi saurin jin gajiya ko ba wata laka.

Mutum ya kasance cikin damuwa ko ya kasance a wani sauyin yanayi, ba zai iya gani sosai ba, idan ya yi rauni ba zai bai warkewa, yasai kuma ta bayyana har ila yau alamu na an kamu, lokacin da mutum yake jin ya kamu da cuta, kamar cutar dasashi, fata da cututtukan Farji da dai sauransu.

Bugu da kari tace yakamata ‘yan Nijeriya da akwai sauran hanyoyin da ake kamuwa da cutar kamar tarihin iyali dangane da cutar siga, yin kiba ko nauyin da ya wuce misali,cin abincin da bai dace ba, rashin motsa jiki, karuwar shekaru, hawan jini, amfani da abincin da bai kamata lokacin da mace take da juna biyu.

Har ila yau da akwai:glucose da tarihin ciwon sukari na ciki suna da alaka da nau’in ciwon sukari na 2, nau’in ciwon siga na 2 wanda shi ne wanda aka fi sani, uwa uba kuma ga tarihin cutar sigar mata masu juna biyu kan kamu da ita.

“Da akwai bukatar kowa ya lura da su wadannan alamun na cutar siga, domin a samu daukar matakain daya kamata saboda san yadda za a kula da cutar da hanyoyin kauce ma kamuwa da ita,bare ma har ma ta kai ga yin kamari.

“Hakanan ma mutane da sduka riga siuka kamu da cutar siga suna da bukatar taimako daga ‘yan’uwansu domin su iya tafiyarda yawan kudaden da ake kashewa wajen kokarin rabuwa da ita, sai kuma irin kallon da za a rika yi masu da su kuma yadda za su ji a jikinsu sanadiyar kamwa da cutar sikari.

Akwai bukatar a rika cin abincin da ya dace musamman ma mai gina jiki, da ci gaba da yawan motsa jiki, ga kuma lura da kada a bari nauyin jiki yayi yawan daya wuce misali.Ana iya duk tafiyar da duk matakan matukar ko wadanne iyalai za su lura da kuma yin amfani da matakan.”

Ta yi kira da ‘yan Nijeriya su san abubbuwan da suka kamata su sani danagane da cutar siga, da hanyoyin kauce ma kamuwa da ita, da mace- macen da ake yi snadiyar cutar.

Wayar da kan al’umma shi ne babban mataki saboda mutanen da suke fama da cutar, da kuma wadanda aka gwada sun kamu da ita amma basu san hanyar da za su bi ba wajen neman maganinta.

Daga karshe Isiabwe tayi kira da gwamnatoci sai masu kula da lafiyar al’umma da masu ruwa da tsaki, su kara zage damtse wajen samar da hanyoyin wayar da kan al’umma yadda za su fahimci al’amarin, hakan zai taimaka masu wajen lura da alamun kamuwa da cutar, da matakan da suka dace na rabuwa ko warkewa daga cutar siga.

Siga
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

MASU ALAKA

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya
Rahotonni

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?
Rahotonni

Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

June 8, 2026
Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana
Rahotonni

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

June 6, 2026
Next Post
Dalibin Da Ya Tsokani Aisha, Zai Gana Da Buhari A Villa

Dalibin Da Ya Tsokani Aisha, Zai Gana Da Buhari A Villa

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.