ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Kula Ga Masu Cutar Siga

by Idris Aliyu Daudawa
4 years ago
Siga

Ciwon Siga wata cuta ce dake da matukar hadari wadda ake kamuwa da ita lokacin da Pancrease wanda wani wuri a kusa da ciki wanda yake samar da sinadarin ‘INSULIN’ da kuma ruwan da yake taimakawa jiki narkar da abinci, ya kasance bai iya samar da sinadarin insulin,ko kuma lokacin da jiki ba zai iya yin amfani da shi.

Har yanzu ita ce cuta da take bada babbar matsala a karni na ashirin da daya, hakan ya kasance ne saboda matsalolin cututtukan da ake kamuwa da su.

  • 2023: Gwamnatinmu Za Ta Farfaɗo Da Harkar ilimi Da Walwalar Malamai – Atiku
  • LP, Ta Kori Daraktan Yakin Neman Zaben Obi, Okupe Da Wasu 11 Kan Gaza Biyan Harajin Jam’iyyar

Shugabar kwamitin amintattu ta wayar da kan al’umma wajen kokarin da ake yi na yakar cutar Dokta Afoke Isiabwe ta bayyana cewa cutar Siga ta shafi mutane kusan milyan 537 da kuma yara fiye da milyan 1.1 a fadin duniya wannan ya hada da ‘yan Nijeriya milyan ko wacce shekara.

ADVERTISEMENT

Duk shekara cutar Siga tana kashe mutane kusan milyan hudu a duniya, ta dai kara jaddada cewa cutar tana iya shafar gaba daya ko wanne sashe na jiki.

Tana sanadiyar rashin gani na idanu, ga matsala mai shafar hakora, tsayawar aikin koda, cardiobascular disease, yanke hannu ko kafa, haduwa da matsala lokacin saduwa da mace, wannan sai idan ba a dauki matakan da suka dace ba.

LABARAI MASU NASABA

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

Tace yawancin abubuwan da cutar siga ta 2 ana iya maganinsu ta hanyar tafiyar da rayuwa yadda ta dace.

Ta bayyana alamun jan kunne na kamuwa da cutar siga da suka hada da lokacin da mutum yake fama jin kishirwa ko shan ruwa,har abin ya wuce kima, ga kuma yawan fitsari, jiki ya kasance babu nauyi saurin jin gajiya ko ba wata laka.

Mutum ya kasance cikin damuwa ko ya kasance a wani sauyin yanayi, ba zai iya gani sosai ba, idan ya yi rauni ba zai bai warkewa, yasai kuma ta bayyana har ila yau alamu na an kamu, lokacin da mutum yake jin ya kamu da cuta, kamar cutar dasashi, fata da cututtukan Farji da dai sauransu.

Bugu da kari tace yakamata ‘yan Nijeriya da akwai sauran hanyoyin da ake kamuwa da cutar kamar tarihin iyali dangane da cutar siga, yin kiba ko nauyin da ya wuce misali,cin abincin da bai dace ba, rashin motsa jiki, karuwar shekaru, hawan jini, amfani da abincin da bai kamata lokacin da mace take da juna biyu.

Har ila yau da akwai:glucose da tarihin ciwon sukari na ciki suna da alaka da nau’in ciwon sukari na 2, nau’in ciwon siga na 2 wanda shi ne wanda aka fi sani, uwa uba kuma ga tarihin cutar sigar mata masu juna biyu kan kamu da ita.

“Da akwai bukatar kowa ya lura da su wadannan alamun na cutar siga, domin a samu daukar matakain daya kamata saboda san yadda za a kula da cutar da hanyoyin kauce ma kamuwa da ita,bare ma har ma ta kai ga yin kamari.

“Hakanan ma mutane da sduka riga siuka kamu da cutar siga suna da bukatar taimako daga ‘yan’uwansu domin su iya tafiyarda yawan kudaden da ake kashewa wajen kokarin rabuwa da ita, sai kuma irin kallon da za a rika yi masu da su kuma yadda za su ji a jikinsu sanadiyar kamwa da cutar sikari.

Akwai bukatar a rika cin abincin da ya dace musamman ma mai gina jiki, da ci gaba da yawan motsa jiki, ga kuma lura da kada a bari nauyin jiki yayi yawan daya wuce misali.Ana iya duk tafiyar da duk matakan matukar ko wadanne iyalai za su lura da kuma yin amfani da matakan.”

Ta yi kira da ‘yan Nijeriya su san abubbuwan da suka kamata su sani danagane da cutar siga, da hanyoyin kauce ma kamuwa da ita, da mace- macen da ake yi snadiyar cutar.

Wayar da kan al’umma shi ne babban mataki saboda mutanen da suke fama da cutar, da kuma wadanda aka gwada sun kamu da ita amma basu san hanyar da za su bi ba wajen neman maganinta.

Daga karshe Isiabwe tayi kira da gwamnatoci sai masu kula da lafiyar al’umma da masu ruwa da tsaki, su kara zage damtse wajen samar da hanyoyin wayar da kan al’umma yadda za su fahimci al’amarin, hakan zai taimaka masu wajen lura da alamun kamuwa da cutar, da matakan da suka dace na rabuwa ko warkewa daga cutar siga.

Siga
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Rayuwar Galadiman Kano Alhaji Tijjani Hashim (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kyamar Baƙi: An Sake Kwaso Ƴan Nijeriya 83 Daga Afirka Ta Kudu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 60 Da Kayan Aiki A Edo
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tsohon Shugaban Ƙasa Jonathan Ya Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Ƙasa 18 A Jihar Bauchi

MASU ALAKA

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Umarnin Kawo Karshen Matsalar Tsaro
Rahotonni

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

September 5, 2026
Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
Rahotonni

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

September 5, 2026
Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
Rahotonni

Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki

September 5, 2026
Next Post
Dalibin Da Ya Tsokani Aisha, Zai Gana Da Buhari A Villa

Dalibin Da Ya Tsokani Aisha, Zai Gana Da Buhari A Villa

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.