• English
  • Business News
Friday, September 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

by Sulaiman
2 hours ago
in Labarai
0
Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ajandar ci gaban da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ke aiwatarwa ta ƙunshi dukkan sassan ƙasar ba tare da nuna ɓangaranci ba, inda ake gudanar da manyan ayyuka da shirye-shirye a faɗin ƙasa.

 

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana haka ne a Abuja ranar Laraba, lokacin da ya karɓi baƙuncin Kwamishinonin Yaɗa Labarai na jihohi 36.

  • Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

“Ya ce: “Ban taɓa ganin inda ake da ayyukan yi amma Shugaban Ƙasa ya ƙi aiwatarwa saboda gwamnan wannan jiha ba ya cikin APC ba. A duk abin da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi, hankalinsa yana kan ɗan Nijeriya ne.”

 

Labarai Masu Nasaba

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

Dangane da cire tallafin man fetur kuwa, ya ce hakan ya bai wa jihohi damar samun kuɗaɗe fiye da da domin aiwatar da ayyuka masu muhimmanci.

 

Ya ce: “Cire tallafin man fetur ya buɗe hanya da ta bai wa dukkan shugabanninku damar aiwatar da ayyuka da kawo wa jama’a amfanin dimokuraɗiyya. Ban ji wani gwamna ba, ko daga jam’iyyarmu ko wata jam’iyya, da ya ce mu dawo da tsohon tsarin.”

 

Idris ya tunatar da cewa kafin Tinubu ya hau mulki, jihohi 27 na fama da biyan albashi, sannan kashi 97 na kuɗaɗen shiga na ƙasa na tafiya wajen biyan bashi. Amma yanzu, a cewarsa, an samu sauyi saboda gyare-gyaren da Shugaban Ƙasa ya aiwatar.

 

Ya ce: “Nijeriya na kan tafiya zuwa ga ci gaba na dindindin da zai amfani kowa. Saƙona, da kuma saƙon da muke da shi a gare ku duka shi ne ku zo ku shiga wannan jirgi domin kai Nijeriya ga inda Shugaban Ƙasa ya yi alƙawarin kai ta, kuma wanda kuke so ku gani a ƙarshe.”

 

Haka kuma, Ministan ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya za ta kai ziyara wasu jihohin Kudu maso Kudu da Arewa maso Gabas domin duba manyan ayyuka tare da tattaunawa da jama’a a matsayin wani ɓangare na tsarin samun ra’ayin jama’a.

 

A nasa jawabin, Shugaban Ƙungiyar Kwamishinonin Yaɗa Labarai, wanda kuma shi ne Kwamishinan Yaɗa Labarai na Jihar Borno, Farfesa Usman Tar, ya ce za su yi aiki tare ba tare da la’akari da jam’iyyun siyasa ba, domin ƙarfafa haɗin kan ƙasa da inganta ƙimomin al’umma.

 

Ya ce: “A gabanka akwai kwamishinoni daga jam’iyyun siyasa daban-daban, daga yankuna daban-daban na ƙasar nan. Saboda haka muna wakiltar sassa daban-daban na tarayyar Nijeriya. Ba mu zo a madadin wata jam’iyya ko wani muradi na kashin kai ba. Mun zo ne bisa wani dandali na ƙasa domin tattauna hanyoyi da dabarun inganta muradinmu na ƙasa, ɗabi’unmu da kuma wayar da kanmu”

 

Ya ƙara da cewa ƙungiyar tasu za ta ci gaba da goyon bayan ma’aikatar wajen yaɗa muhimman kamfen na ƙasa, ciki har da wayar da kai da tarukan tattaunawa da jama’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yara 400,000 Ne Ke Kamuwa Da Cutar Kansa Duk Shekara A Duniya

Next Post

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

Related

Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara
Labarai

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

6 minutes ago
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu
Labarai

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

1 hour ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

2 hours ago
Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba
Labarai

Yara 400,000 Ne Ke Kamuwa Da Cutar Kansa Duk Shekara A Duniya

2 hours ago
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

2 hours ago
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano
Labarai

NDLEA Ta Kama Kwalaben Akuskura Sama Da 8,000 A Kano

3 hours ago
Next Post
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

September 5, 2025
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 5, 2025
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

September 5, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

September 5, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

September 5, 2025
Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

September 5, 2025
Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba

Yara 400,000 Ne Ke Kamuwa Da Cutar Kansa Duk Shekara A Duniya

September 5, 2025
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

September 5, 2025
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Kwalaben Akuskura Sama Da 8,000 A Kano

September 5, 2025
'Yan Bindiga

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.