CRI Hausa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home DAGA BIRNIN SIN

An Shafe Shekaru Biyu Wajen Kawar Da Talauci A Garin Tongan

by CRI Hausa
January 6, 2021
in DAGA BIRNIN SIN
1 min read
An Shafe Shekaru Biyu Wajen Kawar Da Talauci A Garin Tongan
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Renaguli Kerman ta taba shiga cikin jerin masu fama da talauci, tare da sauran magidanta kimanin dubu 1. Daga bisani, ita da iyalinta sun kaura daga yankin tsauni na gundumar Kizilsu Kirghiz mai cin gashin kanta dake jihar Xinjiang zuwa garin Tongan na gundumar Zepu dake yankin Kashgar na jihar Xijiang.

Bayan sun kaura, gwamnatin wurin ta dukufa domin tabbatar da yanayin zaman karko da neman hanyoyin wadata jama’a.
A garin Tongan dake kusa da kogin Yarkand, an shafe shekaru biyu wajen kyautata yanayin gonakin da fadinsu ya kai sama da muraba’in eka 800. Bayan samun gonaki masu kyau, sai jama’ar wurin suka fara raya sana’o’in shuke-shuke da kiwon dabbobi.
Sa’an nan, a shekarar 2020, an kawar da garin Tongan daga kangin talauci baki daya, zaman rayuwar al’umma na ci gaba da kyautatuwa. An kuma gina hanyoyi da dama, ta yadda, al’ummomin ke iya samun Karin damammakin neman aikin yi da samun wadata.
Renaguli Kerman ta ce, yanzu, muna da gonaki, da sabbin gidaje, da kantuna, kuma, yaranmu suna iya zuwa makarantu domin koyon ilmi, a nan gaba za su sami aikin yi. Kasarmu ta samar mana da manufofi masu kyau da amfani, ya kamata mu yi amfani da wannan dama wajen kyautata zaman rayuwarmu. Ta kuma kara da cewa, ta gamsu sosai, kuma tana sa ran ginuwar wata makoma mai haske. (Mai Fassarawa: Maryam Yang)

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Kyakkyawar Jumma’a Tun Daga Laraba Ake Gane Ta

Next Post

Wannan Al’ada Ta Tsawon Shekaru 31 Ta Kara Bayyana Irin Dadadden Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Afirka

RelatedPosts

Matasan Sin Da Afrika Sun Tattauna Da Nufin Inganta Kare Halittu

Matasan Sin Da Afrika Sun Tattauna Da Nufin Inganta Kare Halittu

by CRI Hausa
7 hours ago
0

Matasan Sin da Afrika, sun gudanar da wani taro ta...

Alluran Rigakafin Kasar Sin Sun Sanya Kwarin Gwiwa Kan Yaki Da Annobar COVID-19 A Kasashe Da Yankuna Masu Yawa

Alluran Rigakafin Kasar Sin Sun Sanya Kwarin Gwiwa Kan Yaki Da Annobar COVID-19 A Kasashe Da Yankuna Masu Yawa

by CRI Hausa
7 hours ago
0

Annobar numfashi ta COVID-19 na ci gaba da yaduwa a...

Alluran Rigakafin Cutar COVID-19 Na Kasar Sin Na Taimakawa Kasashe Da Dama Yaki Da Cutar

Alluran Rigakafin Cutar COVID-19 Na Kasar Sin Na Taimakawa Kasashe Da Dama Yaki Da Cutar

by CRI Hausa
7 hours ago
0

A baya-bayan nan, wasu kasashe da yankuna sun amince da...

Next Post
Wannan Al’ada Ta Tsawon Shekaru 31 Ta Kara Bayyana Irin Dadadden Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Afirka

Wannan Al'ada Ta Tsawon Shekaru 31 Ta Kara Bayyana Irin Dadadden Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Afirka

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version