ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sahihanci Ya Sa Kasar Sin Samun Karbuwa A Nahiyar Afirka

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Shahararren kamfanin tantance ra’ayin jama’a na Gallup, ya gabatar da wani sakamakon binciken da ya yi a kwanan baya, inda ya ce kasar Sin ta zarce kasar Amurka, ta zama wadda ta fi tasiri a nahiyar Afirka. Alkaluman da kamfanin ya gabatar sun nuna cewa, ‘yan Afirka da suke goyon bayan kasar Sin, sun karu daga kashi 52% a shekarar 2022, zuwa kashi 58% a shekarar 2023. Yayin da a daya bangaren, masu goyon bayan kasar Amurka suka ragu daga kashi 59% a shekarar 2022, zuwa kashi 56% a bara.

Wannan sakamakon bincike ya yi daidai da sakamakon nazari da wasu hukumomin binciken ra’ayin jama’a na kasashen Afirka, irinsu Afrobarometer mai hedkwata a kasar Ghana, da Ichikowitz Family Foundation dake kasar Afirka ta Kudu, suka gabatar, inda dukkansu suka sanya kasar Sin a gaban kasar Amurka, a fannin samun karbuwa.

  • An Gudanar Da Bikin Musayar Al’adu Tsakanin Sin Da Serbia A Belgrade
  • Matsayar Sin Da Faransa Ta Bayyana Lamirin Bil Adama Na Kare Adalci

Sai dai me ya sa masu goyon bayan kasar Amurka suka ragu? Kamfanin Gallup bai yi wani karin bayani ba. Amma a ganina a kalla akwai dalilai 2.

ADVERTISEMENT

Na farko, kasar ta kan keta adalci a al’amuran duniya. Misali, a rikicin Falasdinu da Isra’aila na wannan karo, kasar Amurka ta yi ta samar da tallafin makamai ga Isra’ila, abin da ya haddasa dorewar rikicin, gami da tsanantar matsalar jin kai, lamarin da ya janyo dimbin suka daga gamayyar kasa da kasa.

Na biyu, yadda kasar ke kallon kanta kamar “baba”, da son tsoma baki cikin harkokin gidan sauran kasashe. Misali, a nahiyar Afirka, kasar Amurka ta nemi hana kasar Uganda zartas da dokar haramta luwadi, da hana kasar Niger kulla hulda da Rasha da Iran, da dai sauransu.

LABARAI MASU NASABA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

Sa’an nan a daya bangaren, dalilin da ya sa kasar Sin kara samun karbuwa a nahiyar Afirka, shi ne yadda ta magance kurakuran da Amurka ta tabka. A cewar wani shehun malami mai suna Adhere Cavince na kasar Kenya, manufar diplomasiyya ta kasar Sin ta jaddada muhimmancin girmama ikon mulkin kai na sauran kasashe, da rashin tsoma baki cikin harkokin gidansu, da kallon kanta a matsayin kawa maimakon babbar kasar dake da karfi. Wadannan manufofi na kasar Sin sun burge kasashen Afirka, wadanda suka dade suna shan wahalar mulkin mallaka, da shisshigin da kasashen yamma suke yi musu.

Cikin wani bayani mai taken ” Me ya sa kasar Sin ta fi kasar Amurka samun karbuwa a nahiyar Afirka?” da Mista Cavince ya rubuta, wanda aka buga cikin jaridar the Nation ta kasar Kenya, ya ce, kasar Sin na dora muhimmanci kan hadin gwiwa a bangaren tattalin arziki, ba tare da gindaya sharadi na siyasa ba, sabanin abun da kasar Amurka ta kan yi, na alakanta tallafi da zuba jari da sharuda na siyasa, irinsu batun hakkin dan Adam, da tsarin da ake bi wajen gudanar da mulki. Ta wannan hanya, kasar Sin ta samar da dimbin damammaki ga kasashen Afirka, na kiyaye tsarinsu na siyasa, gami da neman dabarar raya tattalin arziki, a lokaci guda.

Ban da haka, Mista Cavince ya ambaci hakikanin ci gaban da kasar Sin ta haifar wa nahiyar Afirka. Inda hadin gwiwar “Ziri Daya da Hanya Daya” ya inganta kayayyakin more rayuwa na kasashen Afirka, da ba da damar raya tattalin arziki, da dunkulewar kasashen Afirka waje guda. Kana zuba jari da kasar Sin take yi ya zama muhimmiyar damar samun kudin shiga da guraben aikin yi ga kasashen Afirka. Haka zalika, yadda kasar Sin ke samar da kudin tallafin karatu ga daliban Afirka domin su yi karatu a kasar Sin, ya karfafa cudanya tsakanin al’ummun bangarorin 2, da ba matasan kasashen Afirka damar kara fahimtar kasar Sin. Sa’an nan ta hanyar raba nagartattun fasahohinta, kasar Sin ta zame wa kasashen Afirka muhimmiyar kawar hadin kai, a kokarinsu na neman ci gaban kasa.

Hakika ainihin dalilin da ya sanya kasar Sin daukar wadannan matakai shi ne tunanin kasar na musamman a fannin hadin gwiwa da kasashen Afirka, wato gaskiya, da kauna, da sahihanci, gami da samar da hakikanin sakamako. Idan wata kasa, yayin da take hulda da sauran kasashe, ta iya nuna wani yanayi na daidaito, da rashin yaudara ta akidar siyasa, da kokarin cika alkawarin da ta dauka, da samar da hakikanin alfanu ga sauran kasashe, ta hanyar hadin gwiwar ta moriyar juna, to, ba za a ki kaunarta ba. Saboda haka, za mu iya cewa, wannan ra’ayi na nuna sahihanci, da samar da hakikanin sakamako na kasar Sin, shi ne tushen hulda mai kyau dake tsakaninta da kasashen Afirka.

Bisa haka, za mu iya hasashen cewa, bayan kasar Sin da kasashen Afirka sun kara karfafa hadin kansu na amfanawa juna a kai a kai, huldar dake tsakaninsu ma za ta kara kyautatuwa. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

MASU ALAKA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Next Post
Shugaba Xi Ya Sanar Da Matakai 6 Da Za Su Tallafa Wajen Gina Alumma Mai Makoma Ta Bai Daya Ga Sin Da Serbia

Shugaba Xi Ya Sanar Da Matakai 6 Da Za Su Tallafa Wajen Gina Alumma Mai Makoma Ta Bai Daya Ga Sin Da Serbia

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.