ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sahihanci Ya Sa Kasar Sin Samun Karbuwa A Nahiyar Afirka

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Shahararren kamfanin tantance ra’ayin jama’a na Gallup, ya gabatar da wani sakamakon binciken da ya yi a kwanan baya, inda ya ce kasar Sin ta zarce kasar Amurka, ta zama wadda ta fi tasiri a nahiyar Afirka. Alkaluman da kamfanin ya gabatar sun nuna cewa, ‘yan Afirka da suke goyon bayan kasar Sin, sun karu daga kashi 52% a shekarar 2022, zuwa kashi 58% a shekarar 2023. Yayin da a daya bangaren, masu goyon bayan kasar Amurka suka ragu daga kashi 59% a shekarar 2022, zuwa kashi 56% a bara.

Wannan sakamakon bincike ya yi daidai da sakamakon nazari da wasu hukumomin binciken ra’ayin jama’a na kasashen Afirka, irinsu Afrobarometer mai hedkwata a kasar Ghana, da Ichikowitz Family Foundation dake kasar Afirka ta Kudu, suka gabatar, inda dukkansu suka sanya kasar Sin a gaban kasar Amurka, a fannin samun karbuwa.

  • An Gudanar Da Bikin Musayar Al’adu Tsakanin Sin Da Serbia A Belgrade
  • Matsayar Sin Da Faransa Ta Bayyana Lamirin Bil Adama Na Kare Adalci

Sai dai me ya sa masu goyon bayan kasar Amurka suka ragu? Kamfanin Gallup bai yi wani karin bayani ba. Amma a ganina a kalla akwai dalilai 2.

ADVERTISEMENT

Na farko, kasar ta kan keta adalci a al’amuran duniya. Misali, a rikicin Falasdinu da Isra’aila na wannan karo, kasar Amurka ta yi ta samar da tallafin makamai ga Isra’ila, abin da ya haddasa dorewar rikicin, gami da tsanantar matsalar jin kai, lamarin da ya janyo dimbin suka daga gamayyar kasa da kasa.

Na biyu, yadda kasar ke kallon kanta kamar “baba”, da son tsoma baki cikin harkokin gidan sauran kasashe. Misali, a nahiyar Afirka, kasar Amurka ta nemi hana kasar Uganda zartas da dokar haramta luwadi, da hana kasar Niger kulla hulda da Rasha da Iran, da dai sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Sa’an nan a daya bangaren, dalilin da ya sa kasar Sin kara samun karbuwa a nahiyar Afirka, shi ne yadda ta magance kurakuran da Amurka ta tabka. A cewar wani shehun malami mai suna Adhere Cavince na kasar Kenya, manufar diplomasiyya ta kasar Sin ta jaddada muhimmancin girmama ikon mulkin kai na sauran kasashe, da rashin tsoma baki cikin harkokin gidansu, da kallon kanta a matsayin kawa maimakon babbar kasar dake da karfi. Wadannan manufofi na kasar Sin sun burge kasashen Afirka, wadanda suka dade suna shan wahalar mulkin mallaka, da shisshigin da kasashen yamma suke yi musu.

Cikin wani bayani mai taken ” Me ya sa kasar Sin ta fi kasar Amurka samun karbuwa a nahiyar Afirka?” da Mista Cavince ya rubuta, wanda aka buga cikin jaridar the Nation ta kasar Kenya, ya ce, kasar Sin na dora muhimmanci kan hadin gwiwa a bangaren tattalin arziki, ba tare da gindaya sharadi na siyasa ba, sabanin abun da kasar Amurka ta kan yi, na alakanta tallafi da zuba jari da sharuda na siyasa, irinsu batun hakkin dan Adam, da tsarin da ake bi wajen gudanar da mulki. Ta wannan hanya, kasar Sin ta samar da dimbin damammaki ga kasashen Afirka, na kiyaye tsarinsu na siyasa, gami da neman dabarar raya tattalin arziki, a lokaci guda.

Ban da haka, Mista Cavince ya ambaci hakikanin ci gaban da kasar Sin ta haifar wa nahiyar Afirka. Inda hadin gwiwar “Ziri Daya da Hanya Daya” ya inganta kayayyakin more rayuwa na kasashen Afirka, da ba da damar raya tattalin arziki, da dunkulewar kasashen Afirka waje guda. Kana zuba jari da kasar Sin take yi ya zama muhimmiyar damar samun kudin shiga da guraben aikin yi ga kasashen Afirka. Haka zalika, yadda kasar Sin ke samar da kudin tallafin karatu ga daliban Afirka domin su yi karatu a kasar Sin, ya karfafa cudanya tsakanin al’ummun bangarorin 2, da ba matasan kasashen Afirka damar kara fahimtar kasar Sin. Sa’an nan ta hanyar raba nagartattun fasahohinta, kasar Sin ta zame wa kasashen Afirka muhimmiyar kawar hadin kai, a kokarinsu na neman ci gaban kasa.

Hakika ainihin dalilin da ya sanya kasar Sin daukar wadannan matakai shi ne tunanin kasar na musamman a fannin hadin gwiwa da kasashen Afirka, wato gaskiya, da kauna, da sahihanci, gami da samar da hakikanin sakamako. Idan wata kasa, yayin da take hulda da sauran kasashe, ta iya nuna wani yanayi na daidaito, da rashin yaudara ta akidar siyasa, da kokarin cika alkawarin da ta dauka, da samar da hakikanin alfanu ga sauran kasashe, ta hanyar hadin gwiwar ta moriyar juna, to, ba za a ki kaunarta ba. Saboda haka, za mu iya cewa, wannan ra’ayi na nuna sahihanci, da samar da hakikanin sakamako na kasar Sin, shi ne tushen hulda mai kyau dake tsakaninta da kasashen Afirka.

Bisa haka, za mu iya hasashen cewa, bayan kasar Sin da kasashen Afirka sun kara karfafa hadin kansu na amfanawa juna a kai a kai, huldar dake tsakaninsu ma za ta kara kyautatuwa. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Shugaba Xi Ya Sanar Da Matakai 6 Da Za Su Tallafa Wajen Gina Alumma Mai Makoma Ta Bai Daya Ga Sin Da Serbia

Shugaba Xi Ya Sanar Da Matakai 6 Da Za Su Tallafa Wajen Gina Alumma Mai Makoma Ta Bai Daya Ga Sin Da Serbia

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.