Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya yi Allah-wadai da ƙara taɓarɓarewar tsaro a Nijeriya bayan mutuwar tsohon ɗan majalisar wakilai, Hon. Abba Anas Adamu, wanda rahotanni suka ce ya mutu yana hannun masu garkuwa da mutane bayan an sace shi a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja.
An ce an yi garkuwa da Adamu ne a ranar 3 ga Mayu, 2026, sannan ya rasu bayan kwana tara, a ranar 12 ga Mayu, duk da ƙoƙarin da iyalansa suka yi na ganin an kuɓutar da shi.
Da yake mayar da martani cikin wata sanarwa da mai taimaka masa na musamman kan hulɗa da jama’a, Phrank Shaibu, ya fitar a ranar Talata, Atiku ya bayyana lamarin a matsayin “babban ƙalubalen ƙasa” da kuma “babbar alamar gazawar” gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
“Mutuwarsa wata alama ce mai nuna yadda tsaro ke ci gaba da taɓarɓarewa a ƙarƙashin gwamnatin Tinubu,” in ji tsohon mataimakin shugaban ƙasar.















Discussion about this post