Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya ƙaddamar da wasu sabbin ayyuka a faɗin jihar a ƙarƙashin shirin gwamnatinsa na ‘Building Your Future’.
Ayyukan sun haɗa da sake gina titin Funtua zuwa Katsina da titin tsohuwar kasuwa, waɗanda aka kashe sama da Naira biliyan 6.4 wajen aiwatar da su.
An sanya fitilu masu amfani da hasken rana a kan titunan domin inganta zirga-zirga, tsaro da harkokin kasuwanci.
A Malumfashi, gwamnan ya ƙaddamar da aikin gina titunan cikin gari guda 20 da kuɗinsu ya kai Naira biliyan 10.2.
Haka kuma, ya buɗe cibiyar sarrafa rogo da gari ta zamani a Batsari, inda ya ce za ta taimaka wa manoma, rage asarar amfanin gona bayan girbi da kuma samar da ayyukan yi.
Gwamna Radda, ya kuma duba aikin gina sabuwar makarantar sakandare, ya kuma ƙaddamar da titin cikin garin Batsari, sannan ya buɗe shirin Hukumar Bunƙasa Kasuwanci ta Jihar Katsina (KASEDA) tare da Shirin Tallafa wa Ƙananan ’Yan Kasuwa na UNDP.
Shirin zai samar da kayan sana’o’i da darajarsu ta kai tsakanin Naira 150,000 zuwa 320,000 ga matasa da sauran ’yan kasuwa da suka samu horo, musamman a yankunan da matsalar tsaro ta shafa, domin inganta rayuwa da samar da ayyukan yi.














