Kwanan nan, Wang Yi, mamba a ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin kuma ministan harkokin wajen kasar, ya yi karin haske kan matsayin Sin dangane da batun tekun kudancin Sin, a yayin taron ministocin harkokin wajen Sin da na kasashen kungiyar ASEAN.
Wang Yi ya bayyana cewa, Sin da kasashen ASEAN suna da hikima da kuma karfin iya ci gaba da tafiyar da batun tekun kudancin Sin yadda ya kamata, tare da sanya zaman lafiya, kwanciyar hankali, hadin gwiwa da abota su zama babban jigon batutuwan da suka shafi wannan teku.
Wani bincike ta hanyar jin ra’ayoyin jama’a da kafar CGTN ta babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin (CMG) ta gudanar a tsakanin mutane 2,664 a kasashe shida, da suka hada da Indonesia, Malaysia, Thailand, Vietnam, Philippines da Singapore, a tsakanin watannin Yuni da Yuli na wannan shekara, ya nuna cewa ana kallon tsoma bakin wasu kasashen wajen yankin masu nuna karfin iko a matsayin babban abin da yake haifar da zaman dar-dar a tekun kudancin Sin, kana warware takaddamar tekun cikin lumana kuma ta hannun kasashen yankin bisa cin gashin kansu, shi ne ra’ayi na bai-daya da masu bayyana ra’ayoyin suka yi tarayya a kai.
Musamman ma: Kashi 84.6% na wadanda suka bayyana ra’ayoyinsu sun yi amannar cewa ya kamata a warware takaddamar tekun kudancin Sin ta hanyar tattaunawa cikin lumana da tuntubar juna, bisa dokokin kasa da kasa, inda kuma kashi 64.3% na ganin cewa tsoma bakin kasashen wajen yankin masu nuna karfin iko ya sa wasu kasashen da ke ikirarin mallakar yankin dogaro da taimakon waje, maimakon shiga tattaunawar yankin, lamarin da ke kara raunana karfin yankin na warware takaddama bisa cin gashin kansa.Kazalika, kashi 74.4% na masu bayyana ra’ayoyin sun yi gargadin cewa ci gaba da tsoma bakin kasashen wajen yankin zai kara tsananta zaman dar-dar, lamarin da zai kawo barazana ga cinikayyar duniya da kuma samar da wadataccen makamashi. (Abdulrazaq Yahuza Jere)














