ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 23, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

by Sadiq
24 minutes ago
Trump

Jam’iyyar ADC ta ce wasikar da aka ruwaito shugaban Amurka Donald Trump ya aike wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ba ta nuna cewa gwamnatin Tinubu ta yi nasara, kuma ba za ta taimaka masa ya lashe zaɓe a nan gaba ba.

A cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya fitar a ranar Alhamis, ADC ta ce musayar wasiku tsakanin shugabannin ƙasashe abu ne na al’ada a harkokin diflomasiyya, don haka bai kamata a ɗauke ta a matsayin goyon baya ga gwamnatin Tinubu ba.

Abdullahi ya ce gwamnati na amfani da wannan wasika ne domin neman amincewar jama’a maimakon ta mayar da hankali wajen magance manyan matsalolin da ƙasar ke fuskanta, musamman rashin tsaro.

ADVERTISEMENT

Ya ce har yanzu ‘yan Nijeriya da dama na rayuwa cikin fargaba saboda hare-haren ‘yan bindiga da sace-sacen mutane, yayin da daruruwan mata da yara ke ci gaba da kasancewa a hannun masu garkuwa da mutane a wasu sassan Jihar Borno da Kaiama aJjihar Kwara.

Ya kuma ce gwamnatin Amurka ba ta janye takunkumin da ta sanya wa Njeriya ba.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Amince Da Kafa Sabuwar Bataliyar Sojoji A Jihar Kwara

A cewarsa, har yanzu wasu jihohi na karkashin matakin gargadi na 3 da na 4 saboda matsalolin ta’addanci, garkuwa da mutane, aikata laifuka da rikice-rikicen tsaro.

Abdullahi ya ce hakan ya nuna cewa bai dace a ɗauki wasikar a matsayin hujjar cewa matsalar tsaro a Nijeriya ta inganta ba.

Ya ƙara da cewa ‘yan Nijeriya za su yi wa gwamnatin Tinubu hukunci ne bisa irin sauye-sauyen da ta kawo a rayuwarsu, ba wai saboda wasikun da take karɓa daga shugabannin ƙasashen waje ba.

Ya buƙaci gwamnatin ta mayar da hankali kan samar da sakamako mai anfani ga jama’a maimakon murna game da yabon ƙasashen waje.

MASU ALAKA

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

July 23, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP,  Sun Kashe ’Yan Ta’adda 20 A Yobe
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Amince Da Kafa Sabuwar Bataliyar Sojoji A Jihar Kwara

July 23, 2026
Akpabio
Manyan Labarai

Tinubu Ya Dukufa Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro — Akpabio

July 23, 2026

LABARAI MASU NASABA

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

July 23, 2026
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 25 Da Daddale Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Sada Zumunta A Tsakanin Sin Da Rasha

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 25 Da Daddale Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Sada Zumunta A Tsakanin Sin Da Rasha

July 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio

July 23, 2026
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

July 23, 2026
Sarkin Katagum Ya Jagoranci Addu’ar Roƙon Ruwa A Azare

Sarkin Katagum Ya Jagoranci Addu’ar Roƙon Ruwa A Azare

July 23, 2026
Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?

Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?

July 23, 2026
Cire Tallafi: Majalisar Nasarawa Za Ta Binciki Yadda Aka Karkatar Da Kayan Tallafin Jihar

Gwamnan Nasarawa Ya Sallami Kwamishinoni Shida Na Majalisar Zartarwar Jihar

July 23, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP,  Sun Kashe ’Yan Ta’adda 20 A Yobe

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Amince Da Kafa Sabuwar Bataliyar Sojoji A Jihar Kwara

July 23, 2026
Akpabio

Tinubu Ya Dukufa Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro — Akpabio

July 23, 2026
Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba

Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba

July 22, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.