Jam’iyyar ADC ta ce wasikar da aka ruwaito shugaban Amurka Donald Trump ya aike wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ba ta nuna cewa gwamnatin Tinubu ta yi nasara, kuma ba za ta taimaka masa ya lashe zaɓe a nan gaba ba.
A cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya fitar a ranar Alhamis, ADC ta ce musayar wasiku tsakanin shugabannin ƙasashe abu ne na al’ada a harkokin diflomasiyya, don haka bai kamata a ɗauke ta a matsayin goyon baya ga gwamnatin Tinubu ba.
Abdullahi ya ce gwamnati na amfani da wannan wasika ne domin neman amincewar jama’a maimakon ta mayar da hankali wajen magance manyan matsalolin da ƙasar ke fuskanta, musamman rashin tsaro.
Ya ce har yanzu ‘yan Nijeriya da dama na rayuwa cikin fargaba saboda hare-haren ‘yan bindiga da sace-sacen mutane, yayin da daruruwan mata da yara ke ci gaba da kasancewa a hannun masu garkuwa da mutane a wasu sassan Jihar Borno da Kaiama aJjihar Kwara.
Ya kuma ce gwamnatin Amurka ba ta janye takunkumin da ta sanya wa Njeriya ba.
A cewarsa, har yanzu wasu jihohi na karkashin matakin gargadi na 3 da na 4 saboda matsalolin ta’addanci, garkuwa da mutane, aikata laifuka da rikice-rikicen tsaro.
Abdullahi ya ce hakan ya nuna cewa bai dace a ɗauki wasikar a matsayin hujjar cewa matsalar tsaro a Nijeriya ta inganta ba.
Ya ƙara da cewa ‘yan Nijeriya za su yi wa gwamnatin Tinubu hukunci ne bisa irin sauye-sauyen da ta kawo a rayuwarsu, ba wai saboda wasikun da take karɓa daga shugabannin ƙasashen waje ba.
Ya buƙaci gwamnatin ta mayar da hankali kan samar da sakamako mai anfani ga jama’a maimakon murna game da yabon ƙasashen waje.













