Ƙasashen Mali, Nijar da Burkina Faso, mambobin Ƙungiyar Kawancen Ƙasashen Sahel (AES), sun nuna sha’awar haɗa ƙarfi domin karɓar baƙuncin Gasar Kofin Ƙasashen Afirka (AFCON) ta shekarar 2032.
Matakin ya nuna ƙarin haɗin kai tsakanin ƙasashen uku, bayan da aka tabbatar cewa ƙasashen Kenya, Tanzania da Uganda ne za su karɓi baƙuncin gasar AFCON ta 2027, wadda za a buga daga ranar 19 ga watan Yuni zuwa 17 ga watan Yuli.
Shirin ya samu ci gaba ne bayan jami’ai daga Mali, Nijar da Burkina Faso sun gana da shugaban Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Afirka (CAF), Patrice Motsepe, a birnin New York domin tattauna yiwuwar shirya gasar tare.
A wata sanarwa, Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Mali ta bayyana taron a matsayin “babban mataki”, tana mai cewa hakan zai bai wa ƙasashen uku damar fara cika sharuɗan da CAF ta gindaya domin neman karɓar baƙuncin gasar ta 2032.
Idan ƙasashen uku suka samu damar shirya gasar, Mali za ta sake karɓar baƙuncin AFCON karo na farko tun bayan shekarar 2002.
Burkina Faso kuma za ta karɓi baƙuncin gasar a karon farko tun 1998, yayin da Nijar za ta karɓi bakuncin gasar AFCON a karon farko a tarihinta.
A halin yanzu, Mali na da filayen wasa guda biyar da CAF ta amince da su.
Burkina Faso kuma ta samu amincewar babban filin wasanta da ke Ouagadougou a bara.
Ita kuwa Nijar na ci gaba da gyaran Filin Wasa na Janar Seyni Kountché, wanda CAF ta dakatar da amincewarsa da karɓar wasannin ƙasa da ƙasa tun shekarar 2022.
Sai dai duk da wannan yunƙuri, ƙasashen uku na ci gaba da fuskantar manyan ƙalubalen tsaro da suka shafi hare-haren ƙungiyoyi masu iƙirarin jihadi.














