A jiya Laraba 22 ga wannan wata ne aka gudanar da taron cika shekaru 25 da daddale yarjejeniyar hadin gwiwa, da sada zumunta a tsakanin Sin da Rasha a birnin Harbin dake lardin Heilongjiang na kasar Sin, inda wakilai daga hukumomin da abin ya shafa, da jami’o’i, da kungiyoyin al’adu da na yawon shakatawa, da mata, da kafofin watsa labaru na kasashen biyu kimanin 500 suka halarci taron.Mahalarta taron sun yi imanin cewa, dangantakar dake tsakanin Sin da Rasha ta kasance muhimmin tushe na kiyaye zaman lafiya a duniya, sun kuma yi fatan bangarorin biyu za su kara amincewar juna a fannin siyasa, da yaukaka hadin gwiwar samun moriyar juna, da sada zumunta a tsakanin jama’a, da fadada hadin gwiwar dake tsakanin kasa da kasa, don sa kaimi ga raya dangantaka mai inganci tsakanin Sin da Rasha. (Zainab Zhang)














