Shugaban Amurka Donald Trump, zai ziyarci kasar Sin daga gobe Laraba 13 zuwa Juma’a 15 ga watan nan na Mayu.
Game da hakan, kafar CGTN tare da jami’ar jama’ar Sin, sun gudanar da binciken jin ra’ayin al’umma kan dangantakar Sin da Amurka, wanda masu amsa tambayoyi 12,302 daga kasashe 39 na duniya suka bayar da ra’ayoyinsu.
Sakamakon ya nuna cewa, kaso 75% na masu amsa tambayoyi daga sassan duniya, sun yi imanin cewa dangantakar Sin da Amurka mai inganci da lumana, tana da muhimmanci ga al’ummun duniya.
A cikin masu amsa tambayoyi daga kasashe masu tasowa, wannan adadi ya kai kashi 78.3%, yayin da a cikin masu amsa tambayoyin daga Amurka, kaso 76.7% sun amince da hakan.Kazalika, kaso 67.9% daga cikinsu sun yi imanin cewa Sin da Amurka za su iya cimma nasarar bai daya, kuma za su iya daidaita takaddamar kasuwanci tsakaninsu.
Har ila yau, kaso 74.6% daga cikinsu sun bayyana cewa, ainihin cinikayyar Sin da Amurka, tana amfanar da sassan biyu, kuma hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu yana da amfani ga kowannensu, yayin da yin gaba da juna ke cutar da dukkaninsu.
A daya bangaren kuma, kaso 78.6% sun yi imanin cewa ya kamata Sin da Amurka su karfafa tattaunawa bisa mutunta juna don rage rashin fahimta.
Sai kuma kaso 77.9% da suka yarda cewa “Ya kamata dangantakar kasuwancinsu ta zama mai kwantar da hankali a huldar Sin da Amurka maimakon matakin tayar da rikici.” (Amina Xu)














Discussion about this post