Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
Binciken da cibiyar nazari ta “Pew” ta gudanar ya nuna cewa, a halin yanzu, kasar Sin ta fi kasar Amurka...
Binciken da cibiyar nazari ta “Pew” ta gudanar ya nuna cewa, a halin yanzu, kasar Sin ta fi kasar Amurka...
Ma’aikatar kula da muhallin halittu da muhalli, da kwamitin tsara manufofin raya kasa da aiwatar da sauye-sauye ta kasar Sin,...
"Nuna juriya", da "Wuce tsammani", da "Iya cimma burin ci gaban tattalin arziki na shekara cikin nasara", kalamai ne da...
Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad, ya rushe kwamitin gudanarwar ƙungiyar kwallon ƙafa ta Wikki Tourists nan take, bayan rashin taɓuka...
Sake barkewar hare-hare tsakanin Amurka da Iran a ’yan kwanakin nan ya ja hankalin al’ummun duniya baki daya, tare da hasashen sake dandana mummunan tasirin da yakin zai haifar ga daukacin duniya baki daya idan har ya tsawaita. Duniya na fatan Amurka da Iran za su koma teburin shawarwari ba tare da bata lokaci ba, kana za su kai ga aiwatar da matakan dakatar da zubar da jini cikin hanzari, tare da taka wa yakin birki baki daya. Kasa da wata guda da cimma yarjejeniyar fahimtar juna tsakanin Amurka da Iran, a yanzu tashin hankalin na sake farfadowa. Mun dai ga yadda tun da sanyin safiyar ranar Talata, Amurka ta fara kaddamar da sabbin hare-hare kan sassan Iran cikin kwanaki uku a jere, yayin da ita ma Iran ke mayar da martani kan cibiyoyin aikin soji na Amurka dake kasashen yankinta. Sakamakon wannan dauki ba dadi, tuni farashin mai ya fara hauhawa, kura ta turnuke a mashigin Hormuz, kuma tsarin sufurin hajojin kasuwanci da ya yi matukar rauni a sakamakon tashin hankalin da ya gabata, a yanzu ma ya sake shiga yanayi na ha’ula’i. Masana da dama na cewa, Amurka da Iran ba za su mori wata fa’ida ba daga sake barkewar tashin hankali, kuma dukkanin kasashen duniya za su dandana kudarsu sakamakon sake barkewar tashin hankalin da ake gani a yanzu. Kafin cimma yarjejeniyar fahimtar juna tsakanin sassan biyu, mun ga yadda aka kai ruwa rana wajen tattaunawa, da tuntuba, da shiga tsakani na wasu sassa, har dai aka kai lokacin da Amurka da Iran suka sanar da kawo karshen yaki, da dakatar da daukacin ayyukan soji daga dukkanin fannoni, da kaucewa amfani da karfin soji ta kowane bangare. Sassan biyu sun kuma sha alwashin mutunta ikon mulkin kai da tsaron yankunan juna, tare da kaucewa tsoma hannu cikin harkokin gidan juna. Yanzu haka dai tasirin sake barkewar hare-hare tsakanin Amurka da Iran ya jefa farashin mai cikin yanayi na rashin tabbas, tare da sake gurgunta hada-hadar sufurin hajoji ta mashigin Hormuz, kuma hasashen baya bayan nan na asusun IMF ma, dangane da karuwar ci gaban tattalin arzikin duniya na bana ya ragu da kaso 0.1 bisa dari, kasa da na watan Afirilun da ya shude, inda IMF din ya alakanta hakan kai tsaye da rikicin na gabas ta tsakiya. Alal hakika, duniya ba za ta yi farin ciki da dawowar yaki ba. Kuma sassan kasa da kasa na fatan sassan da rikicin ya shafa za su gaggauta komawa teburin shawarwari, maimakon dauki ba dadi da zai haifar da illa ga dukkanin bangarori. (Saminu Alhassan)
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Lin Jian, ya ce, dangane da babban taron fasahar AI na duniya da taron...
Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya mika wa Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, takardar tabbatar da shi a matsayin abokin...
Yau Alhamis, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gana da shugaban Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev a birnin Shanghai, wanda ya zo kasar don halartar babban taron fasahar AI na duniya da taron manyan jami’ai na duniya kan tafiyar da sha’anin fasahar AI. Bayan ganawar, shugabannin kasashen biyu sun shaida sanya hannu tare da sanar da wasu takardu na hadin gwiwa a fannoni daban-daban, kamar tattalin arziki da ciniki, sufuri, har11kar kudi, da kuma kafofin watsa labarai. Da daren ranar, Xi Jinping da matarsa Peng Liyuan sun shirya wata liyafa a zauren liyafar duniya da ke Shanghai don maraba da manyan baki daga kasa da kasa da za su halarci bikin bude babban taron fasahar AI na duniya da taron manyan jami’ai na duniya kan tafiyar da sha’anin fasahar AI.(Safiyah Ma)
Gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang, a ranar Alhamis ya bukaci Rundunar Sojin Nijeriya da ta daina kallon aikinta a matsayin...
A yau Alhamis, an gudanar da bikin rattaba hannu kan yarjejeniyar kafa kungiyar hadin gwiwar fasahar kirkirarriyar basira ta AI...
© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.
© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.