Binciken da cibiyar nazari ta “Pew” ta gudanar ya nuna cewa, a halin yanzu, kasar Sin ta fi kasar Amurka samun amincewar al’ummomin duniya, kuma wannan shi ne karo na farko da kasar Sin ta zarce Amurka a wannan fanni tun daga shekarar 2023. Haka kuma, binciken ya nuna yadda ra’ayoyin al’ummomin kasashe kawayen kasar Amurka ya canja.
A wani ci gaban kuma, kamfanin dillancin labarai na “Bloomberg News” ya fidda wani labarin dake cewa, a bana binciken da aka yi a kasashe 36, kasar Sin ta fi kasar Amurka samun amincewa a galibin kasashen, wadannan kasashe kuwa sun hada da Canada, da Australia, da Faransa, da Jamus, da ma wasu karin kawayen kasar ta Amurka.
Bugu da kari, kasar Sin ta fi samun amincewa, musamman ma tsakanin kasashen yankin Asiya da Pacifik, da na yankin Gabas ta tsakiya. Cikin kasashen dake wadannan yankuna, kasashe 6 kacal ne suka fi amince da kasar Amurka, wadanda suka hada da kasashen Indiya, da Japan, da Philippines, da Koriya ta Kudu, da Isra’ila da kuma Poland.
A fannin manufar diflomasiyya kuma, kasashe masu samun matsakaicin kudin shiga guda 17, sun fi nuna damuwa kan kasar Amurka, idan aka kwatanta da kasar Sin. Cikin wadannan kasashe, galibinsu sun yi amannar cewa, kasar Sin abokiya ce da suke iya dogaro da ita, kuma akwai karin mutanen dake ganin cewa, idan aka kwatanta da kasar Amurka, Sin ta fi bayar da gudummawar shimfida zaman karko tsakanin kasashen duniya, ko kuma kasashen biyu sun yi daidai wa daida a fannin bayar da gudummawa. (Mai Fassara: Maryam Yang)













